Home General Wani harin mayakan Boko Haram ya yi Sanadiyyar Mayakan ISWAP.

Wani harin mayakan Boko Haram ya yi Sanadiyyar Mayakan ISWAP.

‘Yan Ta’addan kungiyar Boko haram sun fatattaki Mayakan iswap tare da hallaka 35 daga cikin su.

Hare-haren da bangarorin ke ci gaba da kai wa a sansanonin juna wanda kwamandan Boko Haram, ABU UMAIMAH ko BAKOURA DORO ne suka jagoranci kai harin tare da Kwamandoji hudu da wasu mayaka da dama.

Harin da aka fara a Arewacin Kayowa da Toumbun Gini, a Arewa maso Gabashin tafkin Chadi, ya kai ga halaka mayakan ISWAP 35 yayin da wasu da dama suka jikkata.

Zagazola ya rawaito cewa, kwamandan kungiyar Boko Haram maras tausayi ya kuma kwace makamai masu tarin yawa daga hannun ‘yan ta’addar ISWAP, yayin da suka tsere daga sansanonin su.

Majiyar ta bayyana cewa wata babbar kasuwa ta ISWAP dake Toumbun Gini, yan kungiyar JAS ne suka karbe ta a halin yanzu.

Zagazola ya fahimci cewa ‘yan ta’addan da suka tsere abikan gabar tasu sun bi su ne ta kudancin Kangarwa da Dogon Chuku a karamar hukumar Baga.

A makonnin da suka gabata, Yan ta’addan na Boko Haram, sun yi mummunar barna a sansanonin ISWAP da ke dajin Sambisa da kuma yankin tafkin Chadi, lamarin da ya tilastawa ISWAP daukar matakan kariya.

Ko da a ranar 31 ga watan Disamba, an kai hare-hare tsakanin bangarorin ISWAP da JAS da suka dauki tsawon sa’o’i 14 a yankunan Toumbum Allura da Kangar, inda aka kashe mayakan da dama.

Ya bayyana cewa ci gaba da kai hare-hare ya tilastawa mayakan na ISWAP gudanar da taro a Tumbun Murhu tare da manyan shugabannin ISWAP da suka hada da Abubakar Chad, Bashir Ukasha da Abul Kaka- Alias ​​Sa’ad.

Majiyar ta bayyana cewa, manyan batutuwan da aka tattauna a yayin taron su hadar da yadda kungiyarsu ta kasa kai wasu manyan hare-hare a lokacin bukuwan kirsimeti da sabuwar shekara kamar yadda aka tsara tun farko wanda ake dangantawa da fada da hare-haren da mayakan Boko Haram suka kai kan sansanonin ta.

PRNigeria hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 200 Sun Mutu Sakomakon Girgizar ƙasar a ColombiaShahararren Mawaƙin Najeriya, Davido ya Rubuta wa Trump Wasiƙa Kan Zaɓen Jihar OsunHukumar NHRC ta Buƙaci a Kama Malamin Addinin, Sheikh JingirRundunar sojin Najeriya ta Daƙile Shirin Ƴan Bindiga a FilatoJami'an Ƴan Sanda 10 Sun Mutu Yayin Artabu da Ƴan Bindiga a Jihar KebbiAn Naɗa ɗan Najeriya Gidado Shuaib Wakilin Matasa na IPRA-UN Gabanin GWAEFCC da "Wuce Gona da Iri" da Tambayar 2027: Shin ana Rudar da Tinubu ta Hanyar Mutanen da ke Kewaye da Shi ? Daga Yushau A. ShuaibAn Samu Gawar Yara 3 da guda 1 a Sume a Gidan Mai Maganin GargajiyaMene ne Ainihin Abin da ya faru Aka Rufe Asusun Bankunan Gwamnatin Osun ?Jami'an Tsaro Sun Ceto Mutane 308 a Jihohin Arewacin Najeriya An Kama Mutane 6 da Ake Zargin da Taimaka wa Mayaƙan ISWAP a Jihar BornoZaɓen 2027: PDP ta Miƙa Sunan Jonathan ga INEC a Matsayin ɗan Takararta na Shugaban ƙasaIyanen Babban Jami'in Kula da Harkokin Kuɗaɗen ƙungiyar ISWAP Sun Miƙa Wuya ga SojojiAna Zargin Mayaƙan Boko Haram da Kashe Sojojin Nijar 14Gombe 2027: Malamai da Mambobin APC Sun yi Allah-wadai da Sukar Rarara ga Pantami
X whatsapp