Home General NNPC Tana Tafka Asara Wajen Sayar da Mai Saboda Umarnin Gwamnatin Tarayya...

NNPC Tana Tafka Asara Wajen Sayar da Mai Saboda Umarnin Gwamnatin Tarayya Kan Batun Tallafi – Timipre Sylva

Karamin Ministan Fetur a Najeriya ya ce NNPC tana tafka asara wajen sayar da mai saboda umarnin gwamnatin Tarayya kan batun tallafi.

Timipre Sylva ya shaida hakan ne adaidai lokacin da dillalan man fetur ke cewa suna fuskantar karanci mai lamarin da ka iya sake ta’azzara wahalar man har zuwa watan Yuni, saboda shirin gwamnati na janye tallafi baki ɗaya a wannan watan.

An rawaito ministan na waɗannan kalamai ne a yayin da yake bayyana abubuwan da suka aiwatar tsakanin 2015 zuwa 2023 karkashin mulkin Muhammadu Buhari.

A makon da ya gabata, Ministar kuɗi da tsare-tsare, Zainab Ahmed ta ce gwamnati ta ware naira tiriliyan 3.6 na tallafi fetur zuwa Yunin 2023.

An rawaito Sylva a lokacin zantawa da ‘yan jarida a Abuja, na cewa tallafin babban nauyi ne, sai dai kuma wajibi ne ga NNPC da aka daurawa alhakin tafiyar da harkokin fetur a kasar ta ci gaba da daukar asara.

Gwamnatin Najeriya a ranar Litinin ta bayyana cewa ta zuba hannayen jari a matatun mai hudu da ke shirin soma ayyukansu a sassa daban-daban a faɗin Kasar.

PRNigeria hausa

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp