Home General NNPC Tana Tafka Asara Wajen Sayar da Mai Saboda Umarnin Gwamnatin Tarayya...

NNPC Tana Tafka Asara Wajen Sayar da Mai Saboda Umarnin Gwamnatin Tarayya Kan Batun Tallafi – Timipre Sylva

Karamin Ministan Fetur a Najeriya ya ce NNPC tana tafka asara wajen sayar da mai saboda umarnin gwamnatin Tarayya kan batun tallafi.

Timipre Sylva ya shaida hakan ne adaidai lokacin da dillalan man fetur ke cewa suna fuskantar karanci mai lamarin da ka iya sake ta’azzara wahalar man har zuwa watan Yuni, saboda shirin gwamnati na janye tallafi baki ɗaya a wannan watan.

An rawaito ministan na waɗannan kalamai ne a yayin da yake bayyana abubuwan da suka aiwatar tsakanin 2015 zuwa 2023 karkashin mulkin Muhammadu Buhari.

A makon da ya gabata, Ministar kuɗi da tsare-tsare, Zainab Ahmed ta ce gwamnati ta ware naira tiriliyan 3.6 na tallafi fetur zuwa Yunin 2023.

An rawaito Sylva a lokacin zantawa da ‘yan jarida a Abuja, na cewa tallafin babban nauyi ne, sai dai kuma wajibi ne ga NNPC da aka daurawa alhakin tafiyar da harkokin fetur a kasar ta ci gaba da daukar asara.

Gwamnatin Najeriya a ranar Litinin ta bayyana cewa ta zuba hannayen jari a matatun mai hudu da ke shirin soma ayyukansu a sassa daban-daban a faɗin Kasar.

PRNigeria hausa

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Shin AtikuObi Zasu Iya Tsige TinubuShettima a 2027? Daga Yushau A. ShuaibYadda Shari'ar Masarautar Kano ke Ci gaba da Wakana a Kotun ta ƙoliTawagar Amurka na Shirin Tafiya Pakistan Domin Tattaunawar Sulhu da IranDole Najeriya ta Samu Tsaro ta Kowane Hali - Babban Hafsan TsaroChelsea da Newcastle na Harin Coulibaly, Liverpool na Neman Siyan Marcos SensiBadaƙalar $1.3m: Kotu ta ba EFCC izinin Kama Tsohuwar Ministar jin ƙan Najeriya Sadiya FarouqRaphinha ya Magantu kan Fitar da ƙungiyarsa da aka yi Daga Champion LigRundunar sojin Najeriya ta Musanta bai wa Tsofaffin Mayaƙan Boko Haram MakamaiGwamnatin Tarayya ta Sauya Zarge-Zargen da ta ke yi wa MalamiAn Binne Birgediya Janar Braimah da Sauran Sojojin da Boko Haram ta KasheYaƙin Iran: Hauhawar farashin Kaya a Najeriya ya ƙaruAdadin Matasa 'Yan kwaya da Muka Kama a Shekara 5 - NDLEAJam'iyyar ADC ta Kori Nafi'u Bala GombeRigakafin ƙyanda ya Ceci Yara Miliyan 20 a Afirka - Hukumar Lafiya ta Duniya2027 Ita ce Dama ta ƙarshe da zan Fito Takara - Atiku
X whatsapp