Home General NAHCON ta kula yarjejeniya da Saudiya akan yadda aikin hajji 2023 zai...

NAHCON ta kula yarjejeniya da Saudiya akan yadda aikin hajji 2023 zai kasance

Shugaban hukumar kula da aikin hajji ta Nijeriya NAHCON Zikrullah Kulle Hassan ya jagoranci tawagar masu ruwa da tsaki zuwa kasa mai tsarki domin kulla yarjejeniya da hukumomi daban-daban na kasar Saudiya a wani mataki na fara shirye-shiryen aikin hajjin bana.

Bayanin hakan na kunshe cikin wata sanarwa da hukumar NAHCON ta fitar mai dauke da sa hanun mataimakin daraktar yada labanta Musa Uban Dawaki, inda yace manufar ziyar ita tattaunawa da masu ruwa da tsaki akan harkokin aikin Hajji dake kasar tare da kula yarjejeniya akan yadda aikin hajji 2023. zai guduna .

Rahotonni sun bayyana cewar tuni dai karamin ministan harkokin kasashen wajen Najeriya Ambasada Zubairu Dada ya sanya hannu a kan takaddar yarjejeniyar da aka cimma a kasa mai tsarki a madadin Najeriya.

A zantawarsa da manema labarai daga kasa maitarki kwamishinan hukumar mai kula da harkokin kudi da ma’aikata, Alhaji Nura Hassan Yakasai, ya ce hakan yana nufin kokarin da hukumar ke yi a karkashin jagorancin shugabanta Zikrullah Kulle Hassan na tabbatar da cewar aikin Hajjin 2023 ya zarta wadanda ake gudanarwa a baya cikin ikon Allah.
Sannan ya yi karin haske akan manufofin kulla yarjejeniyar da muhimmancin ta ga Najeriya.

Nura Hassan Yakasai, ya ce cikin ikon Allah shirin da NAHCON ke yi a wannan shekara ta nuna za’a samu nasara fiye da yadda ake gabatar shirin gudanar da aikin hajjin a shekaru baya.

Cikin tawagar akwai Karamin Ministan harkokin Kasashen waje na Najeriya Ambasada Zubairu Dada, da shugaban kwamitin harkokin kasashen waje a majalisar dattawa Sanata Adamu Bulkacuwa, sai shugaban kwamitin aikin hajji a majalisar wakilai ta tarayya Abubakar Hassan Na Laraba, kwamishinonin hukumar aikin hajjin gami da yan kwamitin gudanarwata.

PRNigeria hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 200 Sun Mutu Sakomakon Girgizar ƙasar a ColombiaShahararren Mawaƙin Najeriya, Davido ya Rubuta wa Trump Wasiƙa Kan Zaɓen Jihar OsunHukumar NHRC ta Buƙaci a Kama Malamin Addinin, Sheikh JingirRundunar sojin Najeriya ta Daƙile Shirin Ƴan Bindiga a FilatoJami'an Ƴan Sanda 10 Sun Mutu Yayin Artabu da Ƴan Bindiga a Jihar KebbiAn Naɗa ɗan Najeriya Gidado Shuaib Wakilin Matasa na IPRA-UN Gabanin GWAEFCC da "Wuce Gona da Iri" da Tambayar 2027: Shin ana Rudar da Tinubu ta Hanyar Mutanen da ke Kewaye da Shi ? Daga Yushau A. ShuaibAn Samu Gawar Yara 3 da guda 1 a Sume a Gidan Mai Maganin GargajiyaMene ne Ainihin Abin da ya faru Aka Rufe Asusun Bankunan Gwamnatin Osun ?Jami'an Tsaro Sun Ceto Mutane 308 a Jihohin Arewacin Najeriya An Kama Mutane 6 da Ake Zargin da Taimaka wa Mayaƙan ISWAP a Jihar BornoZaɓen 2027: PDP ta Miƙa Sunan Jonathan ga INEC a Matsayin ɗan Takararta na Shugaban ƙasaIyanen Babban Jami'in Kula da Harkokin Kuɗaɗen ƙungiyar ISWAP Sun Miƙa Wuya ga SojojiAna Zargin Mayaƙan Boko Haram da Kashe Sojojin Nijar 14Gombe 2027: Malamai da Mambobin APC Sun yi Allah-wadai da Sukar Rarara ga Pantami
X whatsapp