Home General NAHCON ta kula yarjejeniya da Saudiya akan yadda aikin hajji 2023 zai...

NAHCON ta kula yarjejeniya da Saudiya akan yadda aikin hajji 2023 zai kasance

Shugaban hukumar kula da aikin hajji ta Nijeriya NAHCON Zikrullah Kulle Hassan ya jagoranci tawagar masu ruwa da tsaki zuwa kasa mai tsarki domin kulla yarjejeniya da hukumomi daban-daban na kasar Saudiya a wani mataki na fara shirye-shiryen aikin hajjin bana.

Bayanin hakan na kunshe cikin wata sanarwa da hukumar NAHCON ta fitar mai dauke da sa hanun mataimakin daraktar yada labanta Musa Uban Dawaki, inda yace manufar ziyar ita tattaunawa da masu ruwa da tsaki akan harkokin aikin Hajji dake kasar tare da kula yarjejeniya akan yadda aikin hajji 2023. zai guduna .

Rahotonni sun bayyana cewar tuni dai karamin ministan harkokin kasashen wajen Najeriya Ambasada Zubairu Dada ya sanya hannu a kan takaddar yarjejeniyar da aka cimma a kasa mai tsarki a madadin Najeriya.

A zantawarsa da manema labarai daga kasa maitarki kwamishinan hukumar mai kula da harkokin kudi da ma’aikata, Alhaji Nura Hassan Yakasai, ya ce hakan yana nufin kokarin da hukumar ke yi a karkashin jagorancin shugabanta Zikrullah Kulle Hassan na tabbatar da cewar aikin Hajjin 2023 ya zarta wadanda ake gudanarwa a baya cikin ikon Allah.
Sannan ya yi karin haske akan manufofin kulla yarjejeniyar da muhimmancin ta ga Najeriya.

Nura Hassan Yakasai, ya ce cikin ikon Allah shirin da NAHCON ke yi a wannan shekara ta nuna za’a samu nasara fiye da yadda ake gabatar shirin gudanar da aikin hajjin a shekaru baya.

Cikin tawagar akwai Karamin Ministan harkokin Kasashen waje na Najeriya Ambasada Zubairu Dada, da shugaban kwamitin harkokin kasashen waje a majalisar dattawa Sanata Adamu Bulkacuwa, sai shugaban kwamitin aikin hajji a majalisar wakilai ta tarayya Abubakar Hassan Na Laraba, kwamishinonin hukumar aikin hajjin gami da yan kwamitin gudanarwata.

PRNigeria hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp