Matasan Nijeriya sun Bukaci Godwin Emefele ya sauka daga mukamin sa

Kungiyar Matasa Najeriya sun gudanar da zanga-zanga a harabar babban bankin Najeriya a birnin Abuja.
sun bukaci gwamnan babban bankin Godwin Emefele ya sauka daga mukaminsa bisa kin bayyana gaban hukumomin tsaro domin amsa tambayoyi.
Matasan na dauke da alluna dauke da koken su inda suka bayyaa Emefele matsayin barazana ga tsaro da kuma neman ya sauka ko a dakatar da shi
Haka kuma kungiyar Matasan ta bukaci gwamnan babban bankin ya amsa gayyatar da Rundunar tsaro ta farin kaya DSS ta yi masa na amsa Tambayoyi
Shugaban Matasan Solomon Adodo wanda ya jagoranci zanga-zangar a kofar shiga babban bankin ya ce kungiyar ta sha alwashin ci gaba da zanga-zangar a birnin Abuja da ma kasar baki daya har sai gwamnan babban bankin ya sauka daga mukaminsa
Raahotanni na nuni da cewa an tsaurara matakan tsaro a shedkwatar babban bankin Najeriya.

Kidnapped School Children

Yauri FGC Students, Kebbi
1190 days 9 hours 27 minutes 26 seconds,

Baptist School Students, Kaduna
1172 days 11 hours 8 minutes 51 seconds

Tegina Islamiya Pupils, Niger (Freed)
Spent 88 days from May 30, 2021 - August 26, 2021


Report By: PRNigeria.com

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com