Home General ‘Yan sanda a kano sun kubutar da yaran da akayi garkuwa dasu...

‘Yan sanda a kano sun kubutar da yaran da akayi garkuwa dasu a jihar

Rundunar ‘Yan Sandan Kano ta kama wasu matasa guda biyu da ake zargi da garkuwa da wasu Yara guda 2 har suka nemi a tura musu Naira Miliyan 20 a matsayin kudin Fansa.

Cikin wata sanarwa da jami’in hulda da jama’a na rundunar yan sandan jihar kano DSP Abdullahi Haruna Kiyawa ya fitar, yace rundunar ta yi nasarar kama matasan ne lokacin da suka aikowa da Iyayen yaran da suka sace da wasika mai dauke da lambar wayarsu da Kuma account number domin tura musu kuɗin fansa.

Yace Matasa Masu suna Nura Auwal Mai shekaru 22 mazaunin Rijiyar lemo da abokin sa Abubakar Lawan mai shekaru 22 mazaunin Bachirawa a kano sun bukaci a iyayen yaran da su basu Naira Miliyan 20 a matsayin kuɗin fansa, yayin da daga bisani suka Amince zasu karbi Naira Miliyan 4 kafin su sake su.

Kiyawa yace tuni wadanda ake zargi suka amsa laifin da ake zargin su da aikatawa, kuma kwamishinan ‘yan sandan jihar kano CP Mamman Dauda ya bada umarnin fadada bincike da Kuma gurfanar da su a gaban kotu domin yanke musu hukunci daidai da laifin su.

Kiyawa yace tuni aka ceto yaran wadanda kowannen su bai wuce shekaru 3 zuwa 4 a Wani kango Inda aka ajiye su, bayan sun karbi korafi daga wani Auwal Sale tun a ranar 26 ga watan Janairu 2023.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp