Home General Hukumar NDLEA ta Kama Mai Juna Biyu Kan Kokarin Safarar Miyagun Kwayoyi

Hukumar NDLEA ta Kama Mai Juna Biyu Kan Kokarin Safarar Miyagun Kwayoyi

Wata mata mai dauke da juna biyu ta fada komar NDLEA bayan da tayi kokarin safarar miyagun kwayoyi.

Matar wanda ta kunshe wiwi a cikin kananan rediyo guda biyu, tayi nufin aika kayan Dubai kafin ta shiga hannu.

Jami’an NDLEA na ci gaba da yunkuri wajen dakile sha da fataucin miyagun kwayoyi kamar yadda kakin su na Lagos ya bayyana.

Legas – Jami’an hukumar hana sha da fataucin miyagun kwayoyi (NDLEA) da ke sansanin fita da kaya ta NAHCO shiyyar filin tashi da saukar jiragen sama na Murtala Muhammad, da ke Ikeja, Lagos, sun kama wata mata mai juna biyu, Mrs Sylvester Gloria Onome, ranar Litin, 30 ga watan Janairu, 2023, saboda samun ta da miyagun kwayoyi.

Mai magana da yawun hukumar, Femi Babafemi, ranar Lahadi a Abuja ya ce an kama matar da giram 800 na wiwi da aka boye a cikin kananan rediyo da za a tura Dubai, Hadaddiyar Daular Larabawa, rahoton Vanguard.

Duk a ranar, Hukumar NDLEA ta kuma dakatar da wasu kayan da aka tura jamhuriyyar Congo, Kinshasa, dauke da kwalabe 111 da mayukan shafawa da aka boye kilo 24.50 na ephedrine, wani sinadari da ake amfani da shi wajen hada methamphetamine

PRNigeria hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 200 Sun Mutu Sakomakon Girgizar ƙasar a ColombiaShahararren Mawaƙin Najeriya, Davido ya Rubuta wa Trump Wasiƙa Kan Zaɓen Jihar OsunHukumar NHRC ta Buƙaci a Kama Malamin Addinin, Sheikh JingirRundunar sojin Najeriya ta Daƙile Shirin Ƴan Bindiga a FilatoJami'an Ƴan Sanda 10 Sun Mutu Yayin Artabu da Ƴan Bindiga a Jihar KebbiAn Naɗa ɗan Najeriya Gidado Shuaib Wakilin Matasa na IPRA-UN Gabanin GWAEFCC da "Wuce Gona da Iri" da Tambayar 2027: Shin ana Rudar da Tinubu ta Hanyar Mutanen da ke Kewaye da Shi ? Daga Yushau A. ShuaibAn Samu Gawar Yara 3 da guda 1 a Sume a Gidan Mai Maganin GargajiyaMene ne Ainihin Abin da ya faru Aka Rufe Asusun Bankunan Gwamnatin Osun ?Jami'an Tsaro Sun Ceto Mutane 308 a Jihohin Arewacin Najeriya An Kama Mutane 6 da Ake Zargin da Taimaka wa Mayaƙan ISWAP a Jihar BornoZaɓen 2027: PDP ta Miƙa Sunan Jonathan ga INEC a Matsayin ɗan Takararta na Shugaban ƙasaIyanen Babban Jami'in Kula da Harkokin Kuɗaɗen ƙungiyar ISWAP Sun Miƙa Wuya ga SojojiAna Zargin Mayaƙan Boko Haram da Kashe Sojojin Nijar 14Gombe 2027: Malamai da Mambobin APC Sun yi Allah-wadai da Sukar Rarara ga Pantami
X whatsapp