Home General A karo na 3 Buhari ya sake ganawa da Emefiele,

A karo na 3 Buhari ya sake ganawa da Emefiele,

Shugaba Nijeriya Muhammadu Buhari ya yi wata ganawar sirri da Gwamnan Babban Bankin kasar (CBN) Godwin Emefiele a fadarsa da ke Abuja.

Wannan shi ne karo na uku da gwamnan yake ganawa da shugaban tun bayan matsalar karancin takardar kudin kasar na naira da ta bullo a sakamakon sauyin wasu daga cikin manyan takardun kudin na 200 da 500 da kuma 1,000 da Babban Bankin ya yi.

Bayan wannan ganawar tasu ta uku a Aso Villa, Emefiele, ya ki cewa uffan ga manema labarai lokacin da ya fito.

Bugu da kari babu wata sanarwa daga fadar ko wani jami’i na gwamnati da ya bayyana dalilin ziyarar gwamnan bankin zuwa fadar shugaban kasar.

Sai dai duk da haka ana ganin ba za ta rasa nasaba da halin da kasar ke ciki ba na karancin takardun na naira da abin da wahalhalun da al’ummar kasar suka samu kansu a ciki a dalilin canjin.

Ko a ranar laraba da ta gabata shugaban kasar ya gana da gwamnan bankin bayan Kotun Kolin kasar ta dakatar da wa’adin da bankin ya sanya na daina karbar tsofaffin kudin daga ranar 10 ga watan Fabarairu.

Har sai Kotun ta yanke hukunci ranar Laraba da ke tafe, a kan karar da gwamnonin jihohi uku – na Kaduna da Kwara da kuma Zamfara suka shigar a kan batun canjin kudin.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 200 Sun Mutu Sakomakon Girgizar ƙasar a ColombiaShahararren Mawaƙin Najeriya, Davido ya Rubuta wa Trump Wasiƙa Kan Zaɓen Jihar OsunHukumar NHRC ta Buƙaci a Kama Malamin Addinin, Sheikh JingirRundunar sojin Najeriya ta Daƙile Shirin Ƴan Bindiga a FilatoJami'an Ƴan Sanda 10 Sun Mutu Yayin Artabu da Ƴan Bindiga a Jihar KebbiAn Naɗa ɗan Najeriya Gidado Shuaib Wakilin Matasa na IPRA-UN Gabanin GWAEFCC da "Wuce Gona da Iri" da Tambayar 2027: Shin ana Rudar da Tinubu ta Hanyar Mutanen da ke Kewaye da Shi ? Daga Yushau A. ShuaibAn Samu Gawar Yara 3 da guda 1 a Sume a Gidan Mai Maganin GargajiyaMene ne Ainihin Abin da ya faru Aka Rufe Asusun Bankunan Gwamnatin Osun ?Jami'an Tsaro Sun Ceto Mutane 308 a Jihohin Arewacin Najeriya An Kama Mutane 6 da Ake Zargin da Taimaka wa Mayaƙan ISWAP a Jihar BornoZaɓen 2027: PDP ta Miƙa Sunan Jonathan ga INEC a Matsayin ɗan Takararta na Shugaban ƙasaIyanen Babban Jami'in Kula da Harkokin Kuɗaɗen ƙungiyar ISWAP Sun Miƙa Wuya ga SojojiAna Zargin Mayaƙan Boko Haram da Kashe Sojojin Nijar 14Gombe 2027: Malamai da Mambobin APC Sun yi Allah-wadai da Sukar Rarara ga Pantami
X whatsapp