INEC ta sake Matsaya kan ajiye muhimman kayan zabe a CBN

Hukumar zaben Najeriya, INEC, ta ce za ta adana muhimman kayan zaben 2023 a Babban Bankin kasar, bayan da a baya ta ce ba za ta yi hakan ba.

Idan dai ba a manta ba a 2022 sakamakon damuwa da jama’a da kungiyoyi suka nuna da kuma matsin lamba da aka yi wa hukumar ta INEC, kan adana kayan a CBN, bayan da Gwamnan bankin Godwin Emefiele ya nuna sha’awarsa ta yin takarar shiugabancin kasar, hukumar ta nuna cewa ba za ta ajiye kayan a can ba.

Shugaban hukumar zaben Farfesa Mahmood Yakubu, a ranar 4 ga watan Yuni 2022, ya ce ba za a kai muhimman kayan zaben CBN ba.

A ranar Talata ne Kwamishinan yada labarai da wayar da kan masu zabe na hukumar ta INEC Festus Okoye ya bayyana cewa wasu daga cikin muhimman kayan zaben suna Babban Bankin, kamar yadda jaridar Punch ta ruwaito.

Okoye ya ce yuni hukumar ta samar tare da kai muhimman kayan zaben kamar su takardar rubuta sakamako da takardar zabe kuma ta adana su a bankin inda daga can za ta kai su ofisoshin INEC da ke kananan hukumomin kasar.

PRNigeria hausa

Kidnapped School Children

Yauri FGC Students, Kebbi
1190 days 13 hours 49 minutes 39 seconds,

Baptist School Students, Kaduna
1172 days 15 hours 31 minutes 4 seconds

Tegina Islamiya Pupils, Niger (Freed)
Spent 88 days from May 30, 2021 - August 26, 2021


Report By: PRNigeria.com

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com