Home General Canjin kuɗi : Kotun Ƙoli ta ɗage zama zuwa ranar Laraba 22...

Canjin kuɗi : Kotun Ƙoli ta ɗage zama zuwa ranar Laraba 22 ga watan Fabarairu

Kotun Ƙolin Najeriya ta ɗage zaman sauraren shari’ar da wasu gwamnonin jihohin ƙasar suka shigar kan ci gaba da amfani da tsofaffin kuɗin ƙasar na takardar naira 200 da 500 da 1,000.

Kotun ta ɗage zaman ne bayan da wasu jihohi guda tara suka bi sahun gwamnonin jihohin Kaduna da Kogi da kuma Zamfara waɗanda suka shigar da ƙarar tun da farko.

Jihohin da ke ɓangaren masu ƙarar bayan guda ukun na farko su ne Kano da Katsina da Sokoto da Lagos da Ondo da Ogun da Ekiti da Rivers.

Ita ma a ɓangarenta gwamnatin ƙasar ta samu jihohin Edo da Bayelsa a matsayin waɗanda ke kare kai a shariar.

Gwamnan jihar Kaduna Mallam Nasir El-Rufai da takwaransa na jihar Kogi Yahaya Bello sun halarci Kotun a yau.

Yanzu dai al’ummar Najeriya za su ci gaba da jira har zuwa 22 ga watan Na Fabrairu kafin sanin matsaya game da ci gaba da amfani da tsofaffin takardun kuɗin ko kuma a’a.

Gwamnatocin jihohin Kaduna, da Zamfa da kuma Kogi ne suka shigar da ƙarar, inda tun farko kotun ta bayar da umurnin jingine wa’adin daina amfani da takardun kuɗin na 10 ga watan Fabrairu, wanda bankin ya bayar a farko.

Mutane dai a Najeriya sun shiga ruɗani a kan ko za su iya ci gaba da amfani da tsofaffin takardun kuɗin na naira 1,000, da 500, da 200 duk da umurnin da kotu ta bayar na jingine wa’adin na 10 ga watan Fabrairu.

Haka nan rahotanni daga wurare da dama sun nuna cewa bankuna sun daina karɓar tsofaffin takardun kuɗin, suna bayar da hujjar cewa umurni ne suka samu daga Babban Bankin na Najeriya.

Bugu da ƙari wasu masu ƙananan sana’o’in da dama sun daina amsar tsofaffin kuɗaɗen.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Dangote ya ƙara farashin man feturHukumar Jin dadin alhazan Kano ta sanar da ranar fara jigilar maniyatantaYadda Lakurawa suka kashe masallata a KebbiDSS ta kama jagoran ISWAP da ake nema ruwa a jallo a EdoBa mu taɓa goyon bayan musguna wa Kristoci ba - Gwamnatin NajeriyaGobara ta tashi a babban kasuwar Fika da ke jihar YobeWaye Tunji Disu: Sabon Babban Sifeton 'Yansandan NajeriyaNijar ta amince da kundin ayyukan AES na shekara ta biyuAtiku ya zargi gwamnatin Tinubu da yi wa dimokuraɗiyya zagon ƙasaGwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanci
X whatsapp