An tabbatar da Mutuwar Sojojin Burkina Faso 50 sakamakon wani harin

Akalla sojojin Burkina Faso 51 ne aka tabbatar da cewa sun rasa rayukansu yayin da wasu da dama suka samu raunuka, sakamakon wani harin kwanton bauna da ‘yan ta’adda suka kai wa dakaru a yankin Sahel kamar dai yadda rundunar sojin kasar ta sanar a wannan litinin.

Wannan lamari dai ya faru ne a ranar juma’a da ta gabata, inda da farko aka ruwaito cewa sojoji 8 ne suka rasa rayukansu, kafin wata sanarwa da rundunar sojin kasar ta fitar a wannan litinin ta bayyana gano karin gawarwakin wasu 43 a inda lamarin ya faru.

Sanarwar ta ci gaba da cewa an kashe ‘yan ta’adda akalla 167, bayan da rundunar sojin saman kasar ta kai daukin gaggawa domin taimaka wa dakarunta.

Hakazalika sanarwar ta ce an lalata ko kuma kwace makamai da kuma babura masu tarin yawa wadanda ‘yan ta’addan ke amfani da su a gumurzun da aka yi tsakanin garuruwan Deou da Oursi da ke yakin na Sahel.

Burkina Faso dai ta jima tana fama da hare-haren masus ikirarin jihadi musamman a yankin Arewaci da kuma gabashin kasar, yayin da wannan barazana ke ci gaba da yaduwa hatta a wasu yankuna da ke kudancin kasar iyaka da Jamhuriyar Benin, Togo da kuma Ghana.

PRNigeria hausa

Kidnapped School Children

Yauri FGC Students, Kebbi
1190 days 14 hours 50 minutes 29 seconds,

Baptist School Students, Kaduna
1172 days 16 hours 31 minutes 54 seconds

Tegina Islamiya Pupils, Niger (Freed)
Spent 88 days from May 30, 2021 - August 26, 2021


Report By: PRNigeria.com

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com