EFCC ta ce ta kai jami’anta wuraren zaɓe domin sanya ido kan ayyukan zaɓen 2023

Hukumar yaƙi da yi wa tattalin arziƙin ƙasa ta’annati EFCC ta ce ta kai jami’anta wuraren zaɓe domin sanya ido kan ayyukan zaɓen, ta kuma bayar da lambobin wayar da za a riƙa buga mata domin ko ta kwana.

EFCC ta wallafa haka ne a shafinta na Twitter inda ta bayyana lambobin wayar da za a riƙa kiranta kai tsaye da an ga wani abu mai kama da laifukan kudi a yayin zaɓe.

A wani ɓangare na tabbatar da an yi zaɓukan shugaban ƙasa da na ‘yan majalisa salin alin shi yasa EFCC ta kai ma’aikatan nata.

Tana so ta tabbatar da an yi zaɓen babu cuta babu cutarwa shi yasa za ta sanya ido kan yadda ake sayan kuri’a wani abu da ya zama ruwan dare a siyasar Najeriya, ko kuma bai wa jami’an da ke aiki kuɗi su ɗauke kai a gudanar da wani abu da bai dace ba.

PRNigeria hausa

Kidnapped School Children

Yauri FGC Students, Kebbi
1190 days 18 hours 33 minutes 56 seconds,

Baptist School Students, Kaduna
1172 days 20 hours 15 minutes 21 seconds

Tegina Islamiya Pupils, Niger (Freed)
Spent 88 days from May 30, 2021 - August 26, 2021


Report By: PRNigeria.com

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com