Home General EFCC ta ce ta kai jami’anta wuraren zaɓe domin sanya ido kan...

EFCC ta ce ta kai jami’anta wuraren zaɓe domin sanya ido kan ayyukan zaɓen 2023

Hukumar yaƙi da yi wa tattalin arziƙin ƙasa ta’annati EFCC ta ce ta kai jami’anta wuraren zaɓe domin sanya ido kan ayyukan zaɓen, ta kuma bayar da lambobin wayar da za a riƙa buga mata domin ko ta kwana.

EFCC ta wallafa haka ne a shafinta na Twitter inda ta bayyana lambobin wayar da za a riƙa kiranta kai tsaye da an ga wani abu mai kama da laifukan kudi a yayin zaɓe.

A wani ɓangare na tabbatar da an yi zaɓukan shugaban ƙasa da na ‘yan majalisa salin alin shi yasa EFCC ta kai ma’aikatan nata.

Tana so ta tabbatar da an yi zaɓen babu cuta babu cutarwa shi yasa za ta sanya ido kan yadda ake sayan kuri’a wani abu da ya zama ruwan dare a siyasar Najeriya, ko kuma bai wa jami’an da ke aiki kuɗi su ɗauke kai a gudanar da wani abu da bai dace ba.

PRNigeria hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Dangote ya ƙara farashin man feturHukumar Jin dadin alhazan Kano ta sanar da ranar fara jigilar maniyatantaYadda Lakurawa suka kashe masallata a KebbiDSS ta kama jagoran ISWAP da ake nema ruwa a jallo a EdoBa mu taɓa goyon bayan musguna wa Kristoci ba - Gwamnatin NajeriyaGobara ta tashi a babban kasuwar Fika da ke jihar YobeWaye Tunji Disu: Sabon Babban Sifeton 'Yansandan NajeriyaNijar ta amince da kundin ayyukan AES na shekara ta biyuAtiku ya zargi gwamnatin Tinubu da yi wa dimokuraɗiyya zagon ƙasaGwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanci
X whatsapp