Gwamnan jihar Rivers, Nyesom Wike ya ƙaryata zargin da ake masa

Gwamnan jihar Rivers, Nyesom Wike ya ƙaryata zargin da ake masa cewa ya yi ta yi wa mutane barazana tare da haifar da rikici a yayin babban zaɓen Najeriya da aa gudanar ranar Asabar.

Cikin wata sanarwa da kwamishinan yaɗa labarai na jihar, Chris Finebone ya fitar, Wike ya ce zargin ya fito ne daga “maƙiya masu mugun nufi”.

Ta bayyana cewa Wike ba ya tare da sojoji a tawagarsa musamman a lokacin zaɓe.

A cewar sanarwar, Wike da mai ɗakinsa sun wuce gida ne kai tsaye bayan jefa ƙuri’arsu a ranar zaɓen.

A lokacin da ya isa rumfar zaɓensa, an samu tsaiko kafin ya jefa ƙuri’a saboda na’urar BVAS ba ta yi saurin tantance shi ba.

Kidnapped School Children

Yauri FGC Students, Kebbi
1190 days 11 hours 40 minutes 20 seconds,

Baptist School Students, Kaduna
1172 days 13 hours 21 minutes 45 seconds

Tegina Islamiya Pupils, Niger (Freed)
Spent 88 days from May 30, 2021 - August 26, 2021


Report By: PRNigeria.com

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com