Home Labarai Dan Takarar APC a Jihar kano ya kada Kuri’a a mazabar sa

Dan Takarar APC a Jihar kano ya kada Kuri’a a mazabar sa

Dan takarar gwamnan jihar Kano na jam’iyyar APC Dr Nasiru Yusuf Gawuna ya kaɗa ƙuri’ar a akwatinsa mai lamba 041 a mazabar Gawuna da ke ƙaramar hukumar Nasarawa ta jihar Kano.

Dakta Nasiru Yusuf Gawuna shi ne mataimakin gwamnan jihar Kano, kuma yake yi wa jam’iyyar APC mai mulkin jihar takarar kujerar gwamna.

Har wayau kuma a wata rumfar zaɓe mai lamba 47 da ke Hausawa a karamar hukumar tarauni a jihar Kano an sami tsaikon  harya zuwa ƙarfe 9 na safe mai kaɗa ƙuri’a ɗaya ce kawai ta bayyana a rumfar.

Ita ma ta ce sai da ta yi tafiyar tsawon kilomita huɗu kafin isa rumfar zaɓen kasancewar babu abin hawa.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Shin AtikuObi Zasu Iya Tsige TinubuShettima a 2027? Daga Yushau A. ShuaibYadda Shari'ar Masarautar Kano ke Ci gaba da Wakana a Kotun ta ƙoliTawagar Amurka na Shirin Tafiya Pakistan Domin Tattaunawar Sulhu da IranDole Najeriya ta Samu Tsaro ta Kowane Hali - Babban Hafsan TsaroChelsea da Newcastle na Harin Coulibaly, Liverpool na Neman Siyan Marcos SensiBadaƙalar $1.3m: Kotu ta ba EFCC izinin Kama Tsohuwar Ministar jin ƙan Najeriya Sadiya FarouqRaphinha ya Magantu kan Fitar da ƙungiyarsa da aka yi Daga Champion LigRundunar sojin Najeriya ta Musanta bai wa Tsofaffin Mayaƙan Boko Haram MakamaiGwamnatin Tarayya ta Sauya Zarge-Zargen da ta ke yi wa MalamiAn Binne Birgediya Janar Braimah da Sauran Sojojin da Boko Haram ta KasheYaƙin Iran: Hauhawar farashin Kaya a Najeriya ya ƙaruAdadin Matasa 'Yan kwaya da Muka Kama a Shekara 5 - NDLEAJam'iyyar ADC ta Kori Nafi'u Bala GombeRigakafin ƙyanda ya Ceci Yara Miliyan 20 a Afirka - Hukumar Lafiya ta Duniya2027 Ita ce Dama ta ƙarshe da zan Fito Takara - Atiku
X whatsapp