Home Labarai Rundunar ‘Yan Sanda ta Jihar kano ta haramta bikin murnar lashe zabe

Rundunar ‘Yan Sanda ta Jihar kano ta haramta bikin murnar lashe zabe

Rundunar ‘Yan Sandan Jihar Kano ƙarƙashin jagorancin CP Usaini Mohammed Gumel mai jagorantar harkokin zaɓen da ke gudana a jihar, ta haramta bikin murnar lashe ta hanyar zagaye kan tituna ko makamancin haka wanda ka iya haifar da hargitsi a jihar.

Kwamishinan ya bayyana haka ga manema labarai a yammacin Asabar bayan kammala zagayen da haɗakar rundunonin tsaro da suka gabatar na sa ido bisa yadda dokar Hukumar ‘Yan Sanda ta Ƙasa, ƙarƙashin jagorancin IG Usman Baba Alkali ta ɗora ma kowane kwamishina a faɗin ƙasar a lokacin zaɓen.

CP Gumel ya kuma yaba da yadda jama’a a jihar Kano suka karɓi shawarwari na a yi zaɓe cikin kwanciyar hankali, inda ya ce farkon zagaye da rundunar ta fara da sauran shugabanin jami’an tsaro sun isa wuraren da ake gudanar da zaɓe inda masu zaɓe suka yi farin cikinsu.

“Mun kuma ga ƙananan yara da ba su isa zaɓe ba a cikin guraren zaɓe inda muka ga bai kamata a ce ana barin su ba dan ana iya samu ‘yan sane da yankan aljihu ko kuma wani ɓata-gari ya yi amfani da su wajen tada husuma a lokacin gudanar da zaɓen.

“Ina roƙon jama’ar jihar Kano yadda aka bada haɗin kai wajen kaɗa ƙuri’a, nan ma ina kira da roƙo kan a ƙara bada goyon baya har lokacin da hukumar zaɓe za ta bayyana wanda ya ci zaɓe ya kasance an taya shi murna ta fuskar da ta dace.

Daga ƙarshe, ya yi jan hankali kan duk wanda ya fito murnar lashe zaɓe da manufar cin zarafin wani, ya sani hukuma ba za ta ƙyame shi ba.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 200 Sun Mutu Sakomakon Girgizar ƙasar a ColombiaShahararren Mawaƙin Najeriya, Davido ya Rubuta wa Trump Wasiƙa Kan Zaɓen Jihar OsunHukumar NHRC ta Buƙaci a Kama Malamin Addinin, Sheikh JingirRundunar sojin Najeriya ta Daƙile Shirin Ƴan Bindiga a FilatoJami'an Ƴan Sanda 10 Sun Mutu Yayin Artabu da Ƴan Bindiga a Jihar KebbiAn Naɗa ɗan Najeriya Gidado Shuaib Wakilin Matasa na IPRA-UN Gabanin GWAEFCC da "Wuce Gona da Iri" da Tambayar 2027: Shin ana Rudar da Tinubu ta Hanyar Mutanen da ke Kewaye da Shi ? Daga Yushau A. ShuaibAn Samu Gawar Yara 3 da guda 1 a Sume a Gidan Mai Maganin GargajiyaMene ne Ainihin Abin da ya faru Aka Rufe Asusun Bankunan Gwamnatin Osun ?Jami'an Tsaro Sun Ceto Mutane 308 a Jihohin Arewacin Najeriya An Kama Mutane 6 da Ake Zargin da Taimaka wa Mayaƙan ISWAP a Jihar BornoZaɓen 2027: PDP ta Miƙa Sunan Jonathan ga INEC a Matsayin ɗan Takararta na Shugaban ƙasaIyanen Babban Jami'in Kula da Harkokin Kuɗaɗen ƙungiyar ISWAP Sun Miƙa Wuya ga SojojiAna Zargin Mayaƙan Boko Haram da Kashe Sojojin Nijar 14Gombe 2027: Malamai da Mambobin APC Sun yi Allah-wadai da Sukar Rarara ga Pantami
X whatsapp