Home Labarai Sanata Lado Dan Marke yayi watsi da sakamakon zaben Jihar Katsina

Sanata Lado Dan Marke yayi watsi da sakamakon zaben Jihar Katsina

Dan takarar gwamnan jihar Katsina na babbar jam’iyyar hamayya ta PDP, a zaben da ya gabata, Sanata Yakubu Lado Dan Marke, ya yi watsi da sakamakon zaben da hukumar zabe ta bayyana.

Cikin wata hira da ya yi da BBC, Sanata Lado, ya ce, zabe ne mai cike da magudi, da aringizon kuri’u, da barazana ga masu zabe, da dai duk wani ha’incin da bai taba gani a harkar zabe ba.

Ya ce,” Ba mu gamsu da wannan sakamakon zabe ba tun da mun san ba abin da al’umma suka zaba bane aka bayyana.”

Dan takarar gwamna na jam’iyyar ta PDP, ya ce, yakamata a daina yin zabe kawai a rinka yin nadi, don yana ga hakan ya fi alkhairi.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 200 Sun Mutu Sakomakon Girgizar ƙasar a ColombiaShahararren Mawaƙin Najeriya, Davido ya Rubuta wa Trump Wasiƙa Kan Zaɓen Jihar OsunHukumar NHRC ta Buƙaci a Kama Malamin Addinin, Sheikh JingirRundunar sojin Najeriya ta Daƙile Shirin Ƴan Bindiga a FilatoJami'an Ƴan Sanda 10 Sun Mutu Yayin Artabu da Ƴan Bindiga a Jihar KebbiAn Naɗa ɗan Najeriya Gidado Shuaib Wakilin Matasa na IPRA-UN Gabanin GWAEFCC da "Wuce Gona da Iri" da Tambayar 2027: Shin ana Rudar da Tinubu ta Hanyar Mutanen da ke Kewaye da Shi ? Daga Yushau A. ShuaibAn Samu Gawar Yara 3 da guda 1 a Sume a Gidan Mai Maganin GargajiyaMene ne Ainihin Abin da ya faru Aka Rufe Asusun Bankunan Gwamnatin Osun ?Jami'an Tsaro Sun Ceto Mutane 308 a Jihohin Arewacin Najeriya An Kama Mutane 6 da Ake Zargin da Taimaka wa Mayaƙan ISWAP a Jihar BornoZaɓen 2027: PDP ta Miƙa Sunan Jonathan ga INEC a Matsayin ɗan Takararta na Shugaban ƙasaIyanen Babban Jami'in Kula da Harkokin Kuɗaɗen ƙungiyar ISWAP Sun Miƙa Wuya ga SojojiAna Zargin Mayaƙan Boko Haram da Kashe Sojojin Nijar 14Gombe 2027: Malamai da Mambobin APC Sun yi Allah-wadai da Sukar Rarara ga Pantami
X whatsapp