Home Labarai Gwamnatin Nijeriya ta ayyana ranar fara kidaya

Gwamnatin Nijeriya ta ayyana ranar fara kidaya

Hukumar wayar da kan jama’a ta Najeriya ta ce ranar 3 ga watan Mayu za a fara ƙidayar mutane da kuma ta gidaje.

Cikin wata tattaunawa da ya yi da kamfanmin dillancin labarai na Najeriya, babban daraktan hukumar Garba Abari ne ya bayyana hakan, yana cewa za a yi ƙidayar tsakanin 3 zuwa 5 ga watan na Mayu.

A watan Afrilun 2022 ne, gwamnatin Najeriya ta sanar da cewa za ta shirya ƙidaya da zarar an kammala zaɓuka.

Abari ya ce babu wanda za a bari a baya a wannan aiki, kama daga matan gida da magidanta da yara da sauran mutane.

Ya ce tun farko an samu sauyin lokacin da aka sa ne, biyo bayan ɗage zaɓen gwamnoni da aka yi a Najeriya.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp