Home Labarai An samu karin mutane 142 da zazzabin Lassa ya hallaka a Najeriya

An samu karin mutane 142 da zazzabin Lassa ya hallaka a Najeriya

Hukumar dakile cutuka masu yaduwa ta Najeriya, ta ce cikin kasa da watanni uku, an samu rahoton mutane 784 da suka kamu da zazzabin Lassa, inda mutum 142 suka mutu a jihohin kasar 23.

Hukumar ta bayyana hakan ne a shafinta na yanar gizo, inda ta ce an samu rahoton mutanen da suka kamu da cutar ne, daga watan Janairun 2023 zuwa yanzu.

Haka kuma an samu rahoton bullar cutar ne a jihohin Edo, Ondo, Ebonyi, Bauchi, Taraba, Benue, Rivers, Plateau, da kuma Nasarawa.

NCDC ta ce a jimilla daga mako na 1 zuwa mako na 11, a 2023, an samu rahoton mutuwar mutane 142 daidai da kashi 18.1 cikin 100 wanda ya yi kasa da kashi 18.7 na shekarar 2022.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a KatsinaJami'an Kwastam Biyu sun Rasa Ransu a Fafatawa da LakurawaMatar Aure ta Zuba wa Kishiyarta da 'Ya'yanta Biyu Fetur Tare da Banka Musu Wuta a KanoIna da ƴancin Mu'amala da Kowa ba Tare da La'akari da Jam'iyya ba - WikeAdadin Masu Fama da Cutar Tamowa na ƙaruwa a Najeriya - MSFGwamnatin Yobe ta Sha Alwashin Kawo ƙarshen Hare-Haren Boko Haram
X whatsapp