Home Labarai ‘Yan bindiga sun kashe mutum 34 a sansanin ‘yan gudun hijira da...

‘Yan bindiga sun kashe mutum 34 a sansanin ‘yan gudun hijira da ke Benue

Rahotanni na bayyana cewa ‘Yan bindiga sun hallaka mutane 34 a wani hari da suka kai sansanin ‘yan gudun hijira da ke wata makarantar firamari a ƙauyen Mgaban da ke Ƙaramar Hukumar Benue ta Arewa a ranar Juma’a da daddare.

Wani mazaunin yankin ya shaidawa manema labarai cewa maharan sun isa ƙauyen ne da misalin ƙarfe 9 na daren Juma’a.

Ya ce cikin waɗanda aka kashe akwai wata mata mai ciki da ɗanta sannan kuma da dama sun jikkata.

Ka zalika mai bayar da shawara kan harkokin tsaro na Ƙaramar Hukumar Guma Christopher Waku, ya shaida wa jaridar cewa an kashe mutum 34 yayin da aka jikkata wasu 40 na daban.

Kakakin ‘yan sanda ta jihar SP Catherine Anene, ta tabbatar da faruwar lamarin ta hanyar sakon waya da ta turawa wakilin jiridar, sai dai ba ta yi wani cikakken ƙarin bayani ba.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a KatsinaJami'an Kwastam Biyu sun Rasa Ransu a Fafatawa da LakurawaMatar Aure ta Zuba wa Kishiyarta da 'Ya'yanta Biyu Fetur Tare da Banka Musu Wuta a KanoIna da ƴancin Mu'amala da Kowa ba Tare da La'akari da Jam'iyya ba - WikeAdadin Masu Fama da Cutar Tamowa na ƙaruwa a Najeriya - MSFGwamnatin Yobe ta Sha Alwashin Kawo ƙarshen Hare-Haren Boko Haram
X whatsapp