Home SIYASA INEC ta bai wa Hon. Alhassan Ado Doguwa shaidar sake cin zaɓe

INEC ta bai wa Hon. Alhassan Ado Doguwa shaidar sake cin zaɓe

Hukumar zaɓe mai zaman kanta ta Najeriya ta bai wa Hon. Alhassan Ado Doguwa shaidar sake cin zaɓe a matsayin ɗan majalisar wakilai mai wakiltar mazaɓar tarayya ta Doguwa da Tudun Wada, daga Jihar Kano.

Karo na shida kenan, da Ɗan Majalisar na tarayya ke samun nasarar zuwa majalisar ta wakilai daga Jihar Kano, da ke Arewa Maso Yammacin Najeriya, tun bayan dawowar mulkin dimokraɗiyya a Najeriyar a cikin shekarar 1999.

Tun da farko dai hukumar zaɓe mai zaman kanta ta ƙara (INEC) ta soke nasarar Da Hon. Alhassan Ado Doguwa ya samu, a zaɓen 25 ga watan Fabrairu, saboda jami’in sanar da sakamakon, Farfesa Ibrahim Adamu Yakasai ya ce “tursasa masa” aka yi.

Sai dai, jami’in sanar da sakamakon a zaɓen cike-giɓi na mazaɓar, Farfesa Sani Ibrahim a ranar 15 ga watan Afrilu, ya bayyana Alhassan Doguwa Doguwa a matsayin wanda ya yi nasara da ƙuri’u 41,572 bayan wannan zaɓen lafiya.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a KatsinaJami'an Kwastam Biyu sun Rasa Ransu a Fafatawa da LakurawaMatar Aure ta Zuba wa Kishiyarta da 'Ya'yanta Biyu Fetur Tare da Banka Musu Wuta a KanoIna da ƴancin Mu'amala da Kowa ba Tare da La'akari da Jam'iyya ba - WikeAdadin Masu Fama da Cutar Tamowa na ƙaruwa a Najeriya - MSFGwamnatin Yobe ta Sha Alwashin Kawo ƙarshen Hare-Haren Boko Haram
X whatsapp