NCDC tace Lasser ta hallaka mutane 154 a Nijeriya

Cibiyar Daƙile Cutuka Masu Yaɗuwa ta Najeriya NCDC ta ce cutar zazzaɓin lassa ta halaka mutum 154 a cikin jihohin ƙasar 26 tun farkon shekarar da muke ciki.

A cikin rahoton yanayin cutar da cibiyar ta fitar ranar Litinin, NCDC ta ce a cikin watanni huɗun farko na shekarar 2023, an samu masu ɗauke da cutar 897.

Cibiyar ta ce jihohin da aka samu cutar sun haɗar da Ondo da Edo da Bauchi da Taraba da Benue da Plateau da Ebonyi da Nassarawa da Kogi da Taraba da Gombe da Enugu da Kano da Jigawa da sauransu.

Rahoton ya ce, “tun daga satin farko zuwa 16 a wannan shekarar an samu mutuwar mutum 154”.

NCDC ta ce an samu kashi 72 cikin 100 da cutar a jihohi uku da suka haɗar da Ondo da Edo da kuma Bauchi, inda ka samu kashi 28 daga jihohi 23.

Rahoton ya ce adadin masu ɗauke da cutar ya ƙaru idan aka kwatanta da daidai wannan lokaci a shekarar 2022.

PRNigeria hausa

Kidnapped School Children

Yauri FGC Students, Kebbi
1190 days 13 hours 24 minutes 33 seconds,

Baptist School Students, Kaduna
1172 days 15 hours 5 minutes 58 seconds

Tegina Islamiya Pupils, Niger (Freed)
Spent 88 days from May 30, 2021 - August 26, 2021


Report By: PRNigeria.com

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com