Home Labarai Sojojin Nijeriya sun sake kubutar ‘yan matan Chibok

Sojojin Nijeriya sun sake kubutar ‘yan matan Chibok

Dakarun Sojojin Nijeriya sun sami nasarar sake kubutar da karin ‘yan Matan Chibok tare da hallaka ‘yan Ta’ adda 40 – DHQ

Shalkwatar rundunar sojin Nijeriya tace dakarun hadin Guiwa na Operation HADARIN DAJI, dake aikin samar da tsaron a yankin Arewa maso gabashin Nijeriya, sun sami nasarar kama ‘yan Ta’adda 5 tre da kubutar da fararen hula 121 da suka hadar da yara 72 da mata 49 cikin su akwai ‘yan matan makarantar Chibok 2.

Babban hafsan sojojin kasar Laftanal Janar Lucky Irabor ne ya bayyana  hakan yayin da yake bayyana irin nasarorin da rundunar ta samu kamar yadda aka saba mako mako.

Daraktar yada labaran rundunar Manjo Janar Musa Danmadani yayi jawabi dalla-dalla bisa ayyukan dakarun, inda yace dakarun sojin sama dana kasa dake cikin rundunar Operation HADARIN DAJI dake gudanar da ayyukan su a yankin Arewa maso yammacin kasar sun kama wadanda ake zargin ‘yan bindiga ne masu safar kwayoyi a kauyen Wazata dake karamar hukumar birnin Gwari ta jihar Kaduna.

Haka kuma a Arewa maso gabashi dakarun sun sami nasarar hallaka mayaka Boko Haram dana ISWAP 40, tare da kama 25 wanda suka hadar da masu yi musu safarar kayayyaki da baya ai a lokacin da suka shirya kai hare hare kan kauyuka da dazukan garuruwan Gwoza, Bama, Biu, Kukawa, Monguno, Marte, Damboa, Mobbar da yankunan karamar hukumar Konduga a jihar Borno State.

PRNigeria hausa

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 200 Sun Mutu Sakomakon Girgizar ƙasar a ColombiaShahararren Mawaƙin Najeriya, Davido ya Rubuta wa Trump Wasiƙa Kan Zaɓen Jihar OsunHukumar NHRC ta Buƙaci a Kama Malamin Addinin, Sheikh JingirRundunar sojin Najeriya ta Daƙile Shirin Ƴan Bindiga a FilatoJami'an Ƴan Sanda 10 Sun Mutu Yayin Artabu da Ƴan Bindiga a Jihar KebbiAn Naɗa ɗan Najeriya Gidado Shuaib Wakilin Matasa na IPRA-UN Gabanin GWAEFCC da "Wuce Gona da Iri" da Tambayar 2027: Shin ana Rudar da Tinubu ta Hanyar Mutanen da ke Kewaye da Shi ? Daga Yushau A. ShuaibAn Samu Gawar Yara 3 da guda 1 a Sume a Gidan Mai Maganin GargajiyaMene ne Ainihin Abin da ya faru Aka Rufe Asusun Bankunan Gwamnatin Osun ?Jami'an Tsaro Sun Ceto Mutane 308 a Jihohin Arewacin Najeriya An Kama Mutane 6 da Ake Zargin da Taimaka wa Mayaƙan ISWAP a Jihar BornoZaɓen 2027: PDP ta Miƙa Sunan Jonathan ga INEC a Matsayin ɗan Takararta na Shugaban ƙasaIyanen Babban Jami'in Kula da Harkokin Kuɗaɗen ƙungiyar ISWAP Sun Miƙa Wuya ga SojojiAna Zargin Mayaƙan Boko Haram da Kashe Sojojin Nijar 14Gombe 2027: Malamai da Mambobin APC Sun yi Allah-wadai da Sukar Rarara ga Pantami
X whatsapp