Home Labarai NLC DA TUC sun fasa shiga yajin aiki

NLC DA TUC sun fasa shiga yajin aiki

Rahotannin daga Nijeriya na bayyana cewa Manyan kungiyoyin kwadago biyu a kasar na NLC da TUC sun jingine aniyarsu ta shiga yajin aikin sai baba-ta-gani wanda suka shirya farawa ranar Laraba kan tashin farashin man fetur.

Kungiyoyin biyu sun yanke wannan shawarar ce bayan ganawar da suka yi da bangaren gwamnatin tarayya a fadar shugaban kasa, ranar Litinin.

A makon da ya gabata ne dai kungiyoyin kwadago na Najeriya suka bai wa gwamnatin kasar wa’adin zuwa ranar Talata 6 ga watan Mayu domin ta janye cire tallafin man fetur ko kuma su tsunduma yajin aiki.

Shugaban Majalisar Wakilan Najeriya, Femi Gbajabiamila ne ya sanar da matsayar, wadda shugaban kungiyar kwadago ta kasa NLC, Joe Ajero ya tabbatar, bayan kwashe kimanin sa’oi shida ana tattaunawa tsakanin bangarorin biyu.

Wata sanarwar da shugabannin NLC da TUC suka sanyawa hannu, ta ce daya daga cikin dalilan jingine yajin aikin shi ne bai wa gwamnatin tarayya da bangaren ‘yan kwadago damar kafa wani kwamiti da zai duba batun yin karin albashin ma’aikata da kuma lokacin da za a aiwatar da tsarin.

Haka nan kuma za a duba tsarin bayar da tallafin kudade na Bankin Duniya ta yadda za a sanya masu karanin karfi a ciki.

Daga nan kungiyar kwadagon da gwamnati za su sake duba tsarin gyaran matatun man fetur na kasar ta yadda za a iya kammala gyara su.

Bugu da kari gwamnati za ta samar da tsarin gyara hanyoyin mota da kuma samar da layukan dogo a fadin kasar.

A karshe sanarwar ta ce kungiyar kwadago za ta sake yin wani zama da gwamnatin tarayya a ranar 19 ga watan Yuni domin samar da matsaya kan yadda za a aiwatar da tsare-tsaren da aka cimma.

PRNigeria hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 200 Sun Mutu Sakomakon Girgizar ƙasar a ColombiaShahararren Mawaƙin Najeriya, Davido ya Rubuta wa Trump Wasiƙa Kan Zaɓen Jihar OsunHukumar NHRC ta Buƙaci a Kama Malamin Addinin, Sheikh JingirRundunar sojin Najeriya ta Daƙile Shirin Ƴan Bindiga a FilatoJami'an Ƴan Sanda 10 Sun Mutu Yayin Artabu da Ƴan Bindiga a Jihar KebbiAn Naɗa ɗan Najeriya Gidado Shuaib Wakilin Matasa na IPRA-UN Gabanin GWAEFCC da "Wuce Gona da Iri" da Tambayar 2027: Shin ana Rudar da Tinubu ta Hanyar Mutanen da ke Kewaye da Shi ? Daga Yushau A. ShuaibAn Samu Gawar Yara 3 da guda 1 a Sume a Gidan Mai Maganin GargajiyaMene ne Ainihin Abin da ya faru Aka Rufe Asusun Bankunan Gwamnatin Osun ?Jami'an Tsaro Sun Ceto Mutane 308 a Jihohin Arewacin Najeriya An Kama Mutane 6 da Ake Zargin da Taimaka wa Mayaƙan ISWAP a Jihar BornoZaɓen 2027: PDP ta Miƙa Sunan Jonathan ga INEC a Matsayin ɗan Takararta na Shugaban ƙasaIyanen Babban Jami'in Kula da Harkokin Kuɗaɗen ƙungiyar ISWAP Sun Miƙa Wuya ga SojojiAna Zargin Mayaƙan Boko Haram da Kashe Sojojin Nijar 14Gombe 2027: Malamai da Mambobin APC Sun yi Allah-wadai da Sukar Rarara ga Pantami
X whatsapp