Home Labarai Gwamnatin jihar Kano ta gaggauta magance ayyukan daba a jihar – Majalisa

Gwamnatin jihar Kano ta gaggauta magance ayyukan daba a jihar – Majalisa

Majalisar Dokokin Jihar Kano ta yi Kira ga Gwamnatin Jihar Kano data Umarci Kwamishinan ‘Yan sanda na Jihar da sauran hukumomin tsaro dasu Kai daukin gaggawa Unguwannin dake cikin Dala dake fuskantar matsalolin ‘Yan daba da masu kwace dake damun Yankin tsawon kwanaki.

Kiran ya biyo bayan kudurin da Shugaban Masu Rinjaye na majalisar Kuma wakilin Dala Hon Lawan Hussaini ya gabatar a zauren majalisar inda ya ce tsawon kwanaki batagari sun addabi Unguwannin na Dala da adakawa da kewaye da kwace da sare sare da tashin hankali kala kala a tsakar dare.

A cewar sa lamarin ya damu Al’ummar Yankin da tuni wasu sun fara kaura daga gidajensu saboda tsira da rayukansu kasancewar lamarin na janyo raunata mutane maza da mata..

Wakilin karamar Hukumar Rimin gado da Tofa Hon Muhammad Bello Butu-Butu da wakilin Ungoggo a majalisar Hon Aminu Saadu dana Dambatta da na Garko da Kuma na Takai cikin wadanda suka goyi bayan kudirin..

Shugaban Majalisar dokokin ta Kano Rt Hon Jibril Samaila Falgore ya bayyana amincewar Majalisar..

PRNigeria hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 200 Sun Mutu Sakomakon Girgizar ƙasar a ColombiaShahararren Mawaƙin Najeriya, Davido ya Rubuta wa Trump Wasiƙa Kan Zaɓen Jihar OsunHukumar NHRC ta Buƙaci a Kama Malamin Addinin, Sheikh JingirRundunar sojin Najeriya ta Daƙile Shirin Ƴan Bindiga a FilatoJami'an Ƴan Sanda 10 Sun Mutu Yayin Artabu da Ƴan Bindiga a Jihar KebbiAn Naɗa ɗan Najeriya Gidado Shuaib Wakilin Matasa na IPRA-UN Gabanin GWAEFCC da "Wuce Gona da Iri" da Tambayar 2027: Shin ana Rudar da Tinubu ta Hanyar Mutanen da ke Kewaye da Shi ? Daga Yushau A. ShuaibAn Samu Gawar Yara 3 da guda 1 a Sume a Gidan Mai Maganin GargajiyaMene ne Ainihin Abin da ya faru Aka Rufe Asusun Bankunan Gwamnatin Osun ?Jami'an Tsaro Sun Ceto Mutane 308 a Jihohin Arewacin Najeriya An Kama Mutane 6 da Ake Zargin da Taimaka wa Mayaƙan ISWAP a Jihar BornoZaɓen 2027: PDP ta Miƙa Sunan Jonathan ga INEC a Matsayin ɗan Takararta na Shugaban ƙasaIyanen Babban Jami'in Kula da Harkokin Kuɗaɗen ƙungiyar ISWAP Sun Miƙa Wuya ga SojojiAna Zargin Mayaƙan Boko Haram da Kashe Sojojin Nijar 14Gombe 2027: Malamai da Mambobin APC Sun yi Allah-wadai da Sukar Rarara ga Pantami
X whatsapp