Home Labarai INEC ta shigar da karar Hudu Ari gaban kotu

INEC ta shigar da karar Hudu Ari gaban kotu

Hukumar Zabe Mai Zaman Kanta a Najeriya (INEC) ta shigar da tuhume-tuhume shida a gaban kotu, kan dakataccen kwamishinan zabe na jihar Adamawa, Hudu Yunusa-Ari.

Cikin wata sanarwa da hukumar ta fitar mai dauke da sannun shugaban sashen wayar da kan al’umma na hukumar, Festus Okoye, ta ce an shigar da ƙarar ce a babbar kotun jiha da ke Yola, a jihar Adamawa.

Sanarwar ta kuma tabbatar da samun takardar kammala bincike kan laifukan da suka shafi zabe daga hannun ‘yan sanda, bayan kammala bincike kan laifukan zabe da aka yi a babban zaben na 2023, ciki har da wanda ya shafi Ari.

Sanarwar ta ce, “Kamar yadda sashe na 145 (1) na dokar zabe ta 2022 ya tanadar, laifin da aka aikata a ƙarƙashin dokar za a iya gurfanar da shi a gaban kotun majistare ko kuma babbar kotun jihar da aka aikata laifin, ko kuma babban birnin tarayya, Abuja.

Bayanin ya ƙara da cewa Kotu ta sanya ranar Laraba 12 ga Yulin 2023 don fara shari’ar.

Yunusa-Ari dai ya shiga matsala ne bayan kammala zaben gwamnan jihar Adamawa a ranar 15 ga Afrilun 2023, lokacin da ya bayyana Aisha Dahiru ‘Binani’ ta jam’iyyar APC a matsayin wadda ta lashe zaben da aka gudanar a yayin da ake ci gaba da tattara sakamakon zaben.

PRNigeria hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a KatsinaJami'an Kwastam Biyu sun Rasa Ransu a Fafatawa da LakurawaMatar Aure ta Zuba wa Kishiyarta da 'Ya'yanta Biyu Fetur Tare da Banka Musu Wuta a KanoIna da ƴancin Mu'amala da Kowa ba Tare da La'akari da Jam'iyya ba - WikeAdadin Masu Fama da Cutar Tamowa na ƙaruwa a Najeriya - MSFGwamnatin Yobe ta Sha Alwashin Kawo ƙarshen Hare-Haren Boko Haram
X whatsapp