Home Labarai Gwamnatin Jihar Kano zata samar da doka don masu zubar da Shara

Gwamnatin Jihar Kano zata samar da doka don masu zubar da Shara

Gwamnatin jihar Kano ta bayyana cewa baza ta lamunci zubar da Shara da wasu Al’ummar jihar ke yi ba bisa ka’ida ba.

Shugaban hukumar kwashe shara ta jihar Kano Ambassador Alhaji Ahmadu Haruna Zago ne ya bayyana hakan a yayin da yake ganawa da manema labarai a zagayen gani da ido da yake yi kan yadda aikin kwashe Shara ke cigaba da gudana a wasu sassan jihar.

Dan Zago ya kuma tabbatar da cewa nan gaba kadan gwamnati zata Samar da tsarin da zai Kara jaddada dokar hana zubar da shara barkatai musamman a wuraren da Al’umma ke sake jibgewa sharar bayan gwamnati ta kwashe.

Yace, la’akari da yadda wasu daga cikin al’ummomin da aka kwashe sharar su a kwanakin baya suka sake jibge sharar a wuraren, hakan na nufin dole sai gwamnati ta fito da tsarin da zai karfafa dokar zubar da shara ga al’umma musamman a wuraren da aka tanada domin zubarwa.

Suma wasu daga cikin al’ummomin da aka kwashe sharar dake yankunansu musamman na kan titin Katsina daura da makabartar abbatuwa sun bayyana irin cikakken hadin kan da zasu baiwa gwamnati domin tsaftace Muhallansu da titunansu.

PRNigeria hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 200 Sun Mutu Sakomakon Girgizar ƙasar a ColombiaShahararren Mawaƙin Najeriya, Davido ya Rubuta wa Trump Wasiƙa Kan Zaɓen Jihar OsunHukumar NHRC ta Buƙaci a Kama Malamin Addinin, Sheikh JingirRundunar sojin Najeriya ta Daƙile Shirin Ƴan Bindiga a FilatoJami'an Ƴan Sanda 10 Sun Mutu Yayin Artabu da Ƴan Bindiga a Jihar KebbiAn Naɗa ɗan Najeriya Gidado Shuaib Wakilin Matasa na IPRA-UN Gabanin GWAEFCC da "Wuce Gona da Iri" da Tambayar 2027: Shin ana Rudar da Tinubu ta Hanyar Mutanen da ke Kewaye da Shi ? Daga Yushau A. ShuaibAn Samu Gawar Yara 3 da guda 1 a Sume a Gidan Mai Maganin GargajiyaMene ne Ainihin Abin da ya faru Aka Rufe Asusun Bankunan Gwamnatin Osun ?Jami'an Tsaro Sun Ceto Mutane 308 a Jihohin Arewacin Najeriya An Kama Mutane 6 da Ake Zargin da Taimaka wa Mayaƙan ISWAP a Jihar BornoZaɓen 2027: PDP ta Miƙa Sunan Jonathan ga INEC a Matsayin ɗan Takararta na Shugaban ƙasaIyanen Babban Jami'in Kula da Harkokin Kuɗaɗen ƙungiyar ISWAP Sun Miƙa Wuya ga SojojiAna Zargin Mayaƙan Boko Haram da Kashe Sojojin Nijar 14Gombe 2027: Malamai da Mambobin APC Sun yi Allah-wadai da Sukar Rarara ga Pantami
X whatsapp