Home Labarai Jirgin hirar da Sojin Nijeriya yayi Hadari a Makurdi

Jirgin hirar da Sojin Nijeriya yayi Hadari a Makurdi

Wani jirgin saman horar da sojojin saman Najeriya FT-7NI ya yi hatsari a Makurdi, babban birnin jihar Benue.

Bayanai sun nuna cewa lamarin ya faru ne da yammacin ranar Juma’a, yayin da ake wani aikin horo.

Daraktan hulda da jama’a da yaɗa labarai na rundunar sojin sama ta Najeriya, Air Commodore Edward Gabkwet ya tabbatar da hakan a wata sanarwa da ya fitar ranar Juma’a.

Ya ce matukan jirgi biyu na samun kulawa a asibitin sojojin sama da ke brinin Makurdi.

“An yi sa’a, matukan jirgin biyu da ke cikin jirgin sun tsira daga hatsarin bayan da suka yi nasarar ficewa daga cikin jirgin. Bugu da kari, babu asarar rayuka ko asarar dukiya a inda hatsarin ya faru.

Ya ƙara da cewa a halin da ake ciki, babban hafsan sojin sama na Najeriya, Air Vice Marshal Hassan Abubakar, ya kafa kwamitin bincike domin gano musabbabin hatsarin nan take.

PRNigeria hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a KatsinaJami'an Kwastam Biyu sun Rasa Ransu a Fafatawa da LakurawaMatar Aure ta Zuba wa Kishiyarta da 'Ya'yanta Biyu Fetur Tare da Banka Musu Wuta a KanoIna da ƴancin Mu'amala da Kowa ba Tare da La'akari da Jam'iyya ba - WikeAdadin Masu Fama da Cutar Tamowa na ƙaruwa a Najeriya - MSFGwamnatin Yobe ta Sha Alwashin Kawo ƙarshen Hare-Haren Boko Haram
X whatsapp