Home Labarai Mun kama mayakan IPOB cikin wadanda muka tarwatsa – Sojojin Nijeriya

Mun kama mayakan IPOB cikin wadanda muka tarwatsa – Sojojin Nijeriya

Dakarun sojojin Nijeriya dake bibiyar mayakan da suka tserewa hari a Asaba, sun sami nasarar kame mayakan IPOB dauke da raunikan harbi a jikin su.

Wannan na zuwa ne bayan wani sumame da dakarun sojoji suka kai kan maboyar mayakan na IPOB a ranar asabar,

Ta cikin wata sanarwa da darakta yada labaran rundunar  Birgediya Janar Onyema Nwachukwu ya sake wallafawa a shafin hukumar na twitter, tace dakarun dake bin sahun mayakan na IPOB sun sake samun nasarar kwato makamai.

Idan za’a iya tunawa dakarun sojojin bataliya ta 63 karkashin shiyya ta 6 ta kai wani sumame a Safiya Asabar 22 ga watan Yulin 2023 a wani gungurmin DAJI dake Asaba.

Dakarun sun sami nasarar kama mutum daya dake dauke da rauni a jikin sa, gami da wasu mukamai, babu ran hawa Hudu, bindigu kirar  Double Barrel guns guda hudu, sai alburusan AK 47 guda biyar Magazines, da wasu Albusai na musamman guda 18 masu rai, sai wayoyin hannu guda shifa 6 da  Power bank guda 2, da kuma na’urar sadara kira  Boafeng Communication Radios guda shifa da waya kira Android, sai Computer kirar HP guda daya da tutocin kungiyar IPOB guda goma sha uku da dai sauran su.

PRNigeria hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 200 Sun Mutu Sakomakon Girgizar ƙasar a ColombiaShahararren Mawaƙin Najeriya, Davido ya Rubuta wa Trump Wasiƙa Kan Zaɓen Jihar OsunHukumar NHRC ta Buƙaci a Kama Malamin Addinin, Sheikh JingirRundunar sojin Najeriya ta Daƙile Shirin Ƴan Bindiga a FilatoJami'an Ƴan Sanda 10 Sun Mutu Yayin Artabu da Ƴan Bindiga a Jihar KebbiAn Naɗa ɗan Najeriya Gidado Shuaib Wakilin Matasa na IPRA-UN Gabanin GWAEFCC da "Wuce Gona da Iri" da Tambayar 2027: Shin ana Rudar da Tinubu ta Hanyar Mutanen da ke Kewaye da Shi ? Daga Yushau A. ShuaibAn Samu Gawar Yara 3 da guda 1 a Sume a Gidan Mai Maganin GargajiyaMene ne Ainihin Abin da ya faru Aka Rufe Asusun Bankunan Gwamnatin Osun ?Jami'an Tsaro Sun Ceto Mutane 308 a Jihohin Arewacin Najeriya An Kama Mutane 6 da Ake Zargin da Taimaka wa Mayaƙan ISWAP a Jihar BornoZaɓen 2027: PDP ta Miƙa Sunan Jonathan ga INEC a Matsayin ɗan Takararta na Shugaban ƙasaIyanen Babban Jami'in Kula da Harkokin Kuɗaɗen ƙungiyar ISWAP Sun Miƙa Wuya ga SojojiAna Zargin Mayaƙan Boko Haram da Kashe Sojojin Nijar 14Gombe 2027: Malamai da Mambobin APC Sun yi Allah-wadai da Sukar Rarara ga Pantami
X whatsapp