Home Labarai ‘Yan bindiga sun hallaka mutum daya a jihar Katsina

‘Yan bindiga sun hallaka mutum daya a jihar Katsina

Rundunar ‘yan sandan jihar katsina dake arewa maso yammacin Nijeiya ta tabbatar ta mutuwar mutum daya sakamakon harin da ‘yan bindiga suka kai karamar hukumar Kankia ta jihar.

kakakin hukmar ƴan sandan jihar, ASP Abubakar Aliyu, ne ya tabbatar da faruwar lamarin, inda ya ce tuni ƴan sanda suka fara bincike kan lamarin domin kamo waɗanda ke da hannu a kai harin.

‘yan bindigan sun harbi mutumin ne lokacin da suka kai hari wani rukunin gidaje da ke unguwar low-cost kusa da babban asibitin karamar hukumar a daren Asabar.

Wani ganau ya bayyana cewa ƴan bindigar sun zo ne a kan babura, inda suka yi wa rukunin gidajen dirar miƙiya tare da harbi kan mai uwa da wabi, abin da kuma ya janyo mutuwar mutumin mai suna Alhaji Ibrahim Baraya Solo.

Bayan kashe mutumin ne, sai maharan suka tsere tare da barinsa cikin jini.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a KatsinaJami'an Kwastam Biyu sun Rasa Ransu a Fafatawa da LakurawaMatar Aure ta Zuba wa Kishiyarta da 'Ya'yanta Biyu Fetur Tare da Banka Musu Wuta a KanoIna da ƴancin Mu'amala da Kowa ba Tare da La'akari da Jam'iyya ba - WikeAdadin Masu Fama da Cutar Tamowa na ƙaruwa a Najeriya - MSFGwamnatin Yobe ta Sha Alwashin Kawo ƙarshen Hare-Haren Boko Haram
X whatsapp