Home Labarai Babandede ya bukaci gwamnan Kano ya samar da kasuwar zamani jihar

Babandede ya bukaci gwamnan Kano ya samar da kasuwar zamani jihar

Tsohon Babban Kwantirolan hukumar kula da shige da fice na kasa Immigration, Muhammad Babandede, ya shawarci gwamnatin Kano da ta gina kasuwannin da za’ake hada-hadar kasuwanci da cinikayya na tsawon sa’o’i 24 babu yankewa, domin bunkasa tattalin arziqin jihar.

Muhammad Babandede, ya fadi hakan ne lokacin da yake gabatar da wata lakca mai taken rawar da hukumar kula da shige da fice ta kasa Immigration ke takawa wajen habaka kasuwancin jihar Kano, a wani bangare na bikin cikar hukumar shekaru 60 da kafuwa, wacce hukumar lura da shige da ficen reshan jihar Kano ta shirya a dakin taro na Labanon Club dake Unguwar Bompai.

Yace samar da kasuwannin masu ci tsawon awanni 24 a fadin jihar Kano dake zama cibiyar kasuwancin Najeriya, hakan zai taimaka matuka gaya, wajen samar da tsaro da cire da mummunan tinani a zukatan matasa da kuma bunkasa tattalin arziqin kasa da jiha baki daya.

Daga bisani Tsohon Babban Kwantirolan hukumar kula da shige da ficen na kasa Immigration, Muhammad Babandede, ya bukaci hukumar ta Immigration, reshan jihar Kano dama na sauran jihohin Najeriya da su hada hannu da sarakunan gargajiya don samun nasarar tafiyar da aiyukansu yadda yakamata.

PRNigeria hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp