Home Labarai Babandede ya bukaci gwamnan Kano ya samar da kasuwar zamani jihar

Babandede ya bukaci gwamnan Kano ya samar da kasuwar zamani jihar

Tsohon Babban Kwantirolan hukumar kula da shige da fice na kasa Immigration, Muhammad Babandede, ya shawarci gwamnatin Kano da ta gina kasuwannin da za’ake hada-hadar kasuwanci da cinikayya na tsawon sa’o’i 24 babu yankewa, domin bunkasa tattalin arziqin jihar.

Muhammad Babandede, ya fadi hakan ne lokacin da yake gabatar da wata lakca mai taken rawar da hukumar kula da shige da fice ta kasa Immigration ke takawa wajen habaka kasuwancin jihar Kano, a wani bangare na bikin cikar hukumar shekaru 60 da kafuwa, wacce hukumar lura da shige da ficen reshan jihar Kano ta shirya a dakin taro na Labanon Club dake Unguwar Bompai.

Yace samar da kasuwannin masu ci tsawon awanni 24 a fadin jihar Kano dake zama cibiyar kasuwancin Najeriya, hakan zai taimaka matuka gaya, wajen samar da tsaro da cire da mummunan tinani a zukatan matasa da kuma bunkasa tattalin arziqin kasa da jiha baki daya.

Daga bisani Tsohon Babban Kwantirolan hukumar kula da shige da ficen na kasa Immigration, Muhammad Babandede, ya bukaci hukumar ta Immigration, reshan jihar Kano dama na sauran jihohin Najeriya da su hada hannu da sarakunan gargajiya don samun nasarar tafiyar da aiyukansu yadda yakamata.

PRNigeria hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 200 Sun Mutu Sakomakon Girgizar ƙasar a ColombiaShahararren Mawaƙin Najeriya, Davido ya Rubuta wa Trump Wasiƙa Kan Zaɓen Jihar OsunHukumar NHRC ta Buƙaci a Kama Malamin Addinin, Sheikh JingirRundunar sojin Najeriya ta Daƙile Shirin Ƴan Bindiga a FilatoJami'an Ƴan Sanda 10 Sun Mutu Yayin Artabu da Ƴan Bindiga a Jihar KebbiAn Naɗa ɗan Najeriya Gidado Shuaib Wakilin Matasa na IPRA-UN Gabanin GWAEFCC da "Wuce Gona da Iri" da Tambayar 2027: Shin ana Rudar da Tinubu ta Hanyar Mutanen da ke Kewaye da Shi ? Daga Yushau A. ShuaibAn Samu Gawar Yara 3 da guda 1 a Sume a Gidan Mai Maganin GargajiyaMene ne Ainihin Abin da ya faru Aka Rufe Asusun Bankunan Gwamnatin Osun ?Jami'an Tsaro Sun Ceto Mutane 308 a Jihohin Arewacin Najeriya An Kama Mutane 6 da Ake Zargin da Taimaka wa Mayaƙan ISWAP a Jihar BornoZaɓen 2027: PDP ta Miƙa Sunan Jonathan ga INEC a Matsayin ɗan Takararta na Shugaban ƙasaIyanen Babban Jami'in Kula da Harkokin Kuɗaɗen ƙungiyar ISWAP Sun Miƙa Wuya ga SojojiAna Zargin Mayaƙan Boko Haram da Kashe Sojojin Nijar 14Gombe 2027: Malamai da Mambobin APC Sun yi Allah-wadai da Sukar Rarara ga Pantami
X whatsapp