Home Labarai Dr. M.D Hassan ya dauki nauyi Daliban jihar kano 50 a fannin...

Dr. M.D Hassan ya dauki nauyi Daliban jihar kano 50 a fannin karatun Lafiya

Gwamnatin jihar Kano ta ce, za ta rubanya kokarin da ta ke na inganta harkar Ilimi a  jihar  dake arewa maso yammacin Nijeriya dan ganin an samu Al’umma ta gari.

Gwamnan jihar Injiyiya Abba Kabir Yusuf ne ya bayyana hakan yayin taron bayar da tallafin karatun gaba da sakandire a makarantun lafiya ga daliban karamar hukumar Nassarawa 50 da Hon. Muhammad M.D Hassan ya dauki nauyi, domin koyi da tsarin da gwamnatin jihar kano ke kai

Da yake jawabi Gwamnan jihar kano wanda ya sami wakilcin mai taimaka masa  na musamman a fannin harkokin lafiya Hon Ali Chiranchi, ya ce “daman na daga cikin kudirce-kudirce Gwamnatin Abba, na samar da Ingantaccen Ilimi a jihar Kano”, inda ya kuma ja hankalin daliban da su kasance masu maida hankali akan karatun su.

A nasa jawabin Hon. Muhammad M.D Hassan, wanda shi ne wanda ya dauki nauyin Daliban zuwa makarantun Lafiya, yayin zantawar sa da manema labarai jim kadan bayan kammala taron bayar da tallafin ya ce,  “mun dauki nauyin daliban ne domin kara jaddada aniyar mu na samar da ci gaban Al’umma, kamar yadda Engr. Rabi’u Kwankwaso ya dora mu a kai”.

Sannan Hon. Muhammad M.D, ya ce tallafin karatun na a fannin lafiya, zai ci gaba da kasancewa lokaci zuwa lokaci, dan ganin an ragewa Gwamnati nauyin Dalibai ‘yan asalin Kano dake kan ta.

Tallafin karatun na lafiya dai ya sanya daliban cikin farin duba da yadda suka gaza bayyana farin cikin su, kamar yadda wasu daga cikin daliban suka bayyana.

Harkar Ilimi a Nijeeria dai na daya daga cikin abubuwan dake ciwa Al’ummar kasar tuwo a kwarya wanda hakan ne ma tasa, Gwamnatin Kano, ta dauki nauyin Karatun Dalibai 1001 zuwa kasashen ketare.

A makon da ya gabata ne dai Daliban da Gwamnatin jihar Kano kar-kashin jagorancin Abba Kabir Yusuf, ta tura karatu zuwa kasashen waje, suka fara tashi zuwa makarantun da za suyi karatu.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp