Home Labarai Dr. M.D Hassan ya dauki nauyi Daliban jihar kano 50 a fannin...

Dr. M.D Hassan ya dauki nauyi Daliban jihar kano 50 a fannin karatun Lafiya

Gwamnatin jihar Kano ta ce, za ta rubanya kokarin da ta ke na inganta harkar Ilimi a  jihar  dake arewa maso yammacin Nijeriya dan ganin an samu Al’umma ta gari.

Gwamnan jihar Injiyiya Abba Kabir Yusuf ne ya bayyana hakan yayin taron bayar da tallafin karatun gaba da sakandire a makarantun lafiya ga daliban karamar hukumar Nassarawa 50 da Hon. Muhammad M.D Hassan ya dauki nauyi, domin koyi da tsarin da gwamnatin jihar kano ke kai

Da yake jawabi Gwamnan jihar kano wanda ya sami wakilcin mai taimaka masa  na musamman a fannin harkokin lafiya Hon Ali Chiranchi, ya ce “daman na daga cikin kudirce-kudirce Gwamnatin Abba, na samar da Ingantaccen Ilimi a jihar Kano”, inda ya kuma ja hankalin daliban da su kasance masu maida hankali akan karatun su.

A nasa jawabin Hon. Muhammad M.D Hassan, wanda shi ne wanda ya dauki nauyin Daliban zuwa makarantun Lafiya, yayin zantawar sa da manema labarai jim kadan bayan kammala taron bayar da tallafin ya ce,  “mun dauki nauyin daliban ne domin kara jaddada aniyar mu na samar da ci gaban Al’umma, kamar yadda Engr. Rabi’u Kwankwaso ya dora mu a kai”.

Sannan Hon. Muhammad M.D, ya ce tallafin karatun na a fannin lafiya, zai ci gaba da kasancewa lokaci zuwa lokaci, dan ganin an ragewa Gwamnati nauyin Dalibai ‘yan asalin Kano dake kan ta.

Tallafin karatun na lafiya dai ya sanya daliban cikin farin duba da yadda suka gaza bayyana farin cikin su, kamar yadda wasu daga cikin daliban suka bayyana.

Harkar Ilimi a Nijeeria dai na daya daga cikin abubuwan dake ciwa Al’ummar kasar tuwo a kwarya wanda hakan ne ma tasa, Gwamnatin Kano, ta dauki nauyin Karatun Dalibai 1001 zuwa kasashen ketare.

A makon da ya gabata ne dai Daliban da Gwamnatin jihar Kano kar-kashin jagorancin Abba Kabir Yusuf, ta tura karatu zuwa kasashen waje, suka fara tashi zuwa makarantun da za suyi karatu.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Shin AtikuObi Zasu Iya Tsige TinubuShettima a 2027? Daga Yushau A. ShuaibYadda Shari'ar Masarautar Kano ke Ci gaba da Wakana a Kotun ta ƙoliTawagar Amurka na Shirin Tafiya Pakistan Domin Tattaunawar Sulhu da IranDole Najeriya ta Samu Tsaro ta Kowane Hali - Babban Hafsan TsaroChelsea da Newcastle na Harin Coulibaly, Liverpool na Neman Siyan Marcos SensiBadaƙalar $1.3m: Kotu ta ba EFCC izinin Kama Tsohuwar Ministar jin ƙan Najeriya Sadiya FarouqRaphinha ya Magantu kan Fitar da ƙungiyarsa da aka yi Daga Champion LigRundunar sojin Najeriya ta Musanta bai wa Tsofaffin Mayaƙan Boko Haram MakamaiGwamnatin Tarayya ta Sauya Zarge-Zargen da ta ke yi wa MalamiAn Binne Birgediya Janar Braimah da Sauran Sojojin da Boko Haram ta KasheYaƙin Iran: Hauhawar farashin Kaya a Najeriya ya ƙaruAdadin Matasa 'Yan kwaya da Muka Kama a Shekara 5 - NDLEAJam'iyyar ADC ta Kori Nafi'u Bala GombeRigakafin ƙyanda ya Ceci Yara Miliyan 20 a Afirka - Hukumar Lafiya ta Duniya2027 Ita ce Dama ta ƙarshe da zan Fito Takara - Atiku
X whatsapp