Home SIYASA Atiku ya zargi hukunci kotu da cire yadda ga ‘yan Nijeriya

Atiku ya zargi hukunci kotu da cire yadda ga ‘yan Nijeriya

Jagoran adawar Najeriya, ya nemi gaggauta yi wa tsarin mulkin ƙasar gyaran fuska, don hana kotuna abin da ya kira “fakewa a bayan gaza bin ƙa’idojin shigar da ƙara da muhawarorin shari’a masu rikitarwa, suna tabbatar da zaɓen sata da kuma yin zagon ƙasa ga zaɓen al’umma”.

Atiku Abubakar ya ce wajibi ne a mayar da zaɓe da tattara sakamako ta hanyar laturoni, su zama tilas a Najeriya.

Wannan, wani ɓangare ne na taron manema labarai da shugaban adawar, kuma ɗan takarar jam’iyyar PDP a zaɓen 2023, ya gabatar ranar Litinin a Abuja. Taron na zuwa ne kwana uku, bayan hukuncin kotun ƙoli da ya yi watsi da ƙararsa ta ƙalubalantar nasarar Shugaba Bola Ahmed Tinubu.

Kotun dai ta yi watsi da ƙararrakin da Atiku Abubakar tare da takwaransa na jam’iyyar LP, Peter Obi suka ɗaukaka, inda ta ce ba su da ƙwararan hujjoji.

Atiku ya ce matsayin Kotun Kolin ko da yake, shi ne ƙarshe, amma dai ya bar baya da ƙura mai yawa.

Ya yi zargin cewa hukunce-hukuncen kotunan zaɓe, sun zaizaye yardar da ‘yan Najeriya ke da ita, ga tsarin zaɓe da kuma dimokraɗiyyar Najeriya.

Ya ce yana mamakin wanda zai shawo kan miliyoyin ‘yan Najeriya, su fita su yi zaɓe nan gaba, bayan sun bi layi sun yi rijista bisa tabbacin da INEC ta ba su, amma sai suka ga an sace ƙuri’unsu, tare da bai wa waɗanda ba su zaɓa ba, nasara.

Dan adawan ya ce idan mutane suka daina yarda, kuma suka dawo daga rakiyar zaɓuka, dimokraɗiyya ta durƙushe ke nan. Kuma ta hanyar tabbatarwa da halasta ci gaba da rashin gaskiya a zaɓuka, kotunan Najeriya, na ƙwace ‘yancin masu zaɓe, na zaɓar wa kansu shugabanni.

Ita dai hukumar zaɓe ta ce ta yi zaɓe cikin gaskiya da adalci, kuma sakamakon hukunce-hukunce da aka yanke a kotuna sun nuna cewa INEC ta taka rawar gani.

PRNigeria haus

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
HURIWA ta Soki Ƴan Sanda da NDPC Kan Jinkirin Binciken Zargin Kutse da aka yi wa Bayanan NIPSS da ya Shafi Jami’in Sojan RuwaƳa'yan El-Rufai Sun Shiga Rikici Yayin da Bashir ya Zargi Bello da Shan Muggan Kwayoyi da Cin Amanar suTsaro, Fafutuka da Nauyin Tabbatarwa Daga Mukhtar Ya’u MadobiONSA ta Fitar da Faɗakarwar Tsaro, ta Bukaci Ƴan Najeriya su ƙara Yawan Tsawaita TsaroHukumar DSS ta Dakatar da Shari'ar Sowore Kan Laifukan Intanet Har Sai Bayan Zaben Shugaban Kasa na 2027Gwarzo ya ba da Gudummuwar ₦10m ga Horarwa na Musamman na PRNigeria Bayan ya ba da Gidansa na Abuja Don Cibiyar Koyon Aikin Jarida2027: Bayan Takardu da Sauran Tsoffin Maganganu Marasa Amfani, ‘Yan Najeriya Sun Cancanci Kamfen Din da Ya Dace Da Matsaloli  Daga Kabir AkintayoGwamnati Tarayya ta Bayyana Bas 100 Masu Amfani da Wutar Lantarki Don Rage Wa Ma’aikatan Gwamnati Matsalar SufuriƳan Ta’adda na Amfani da Kafafen Sada Zumunta da Dandamalin Aikin Tura Kuɗi Don Tallafa Wa Ayyukansu — BukartiBinciken Gaskiya na PRNigeria: Ta Karyata Da’awar Tony Elumelu ta Cewa An yi Satar Man Fetur Kashi 97% Kafin Zamanin TinubuMeyasa Mutuwar Bazata Take Daukar Masu Alheri ta Bar Mugaye ? Na Yushau A. ShuaibSojoji Sun Kama Bindigar AK-103 Da Aka Boye a Cikin Jakar Gero, Sun Kama Mutum Uku A ZamfaraSojoji Sun Kama Shahararren Shugaban Ƴan Bindiga, 'Sanusi Maigilas' a Dajin Katsina2027: Yadda Zan Magance Rashin Tsaro, In Magance Matsalolin Tattalin Arziki da Zamantakewa a Kwara — Zakari MohammedLabarin NIPSS Mai Damuwa: Lokacin da Jami'in Sojan Ruwa Ya Cin Zarafin Mawallafi Daga Nuhu Mohammed
X whatsapp