Home SIYASA Atiku ya zargi hukunci kotu da cire yadda ga ‘yan Nijeriya

Atiku ya zargi hukunci kotu da cire yadda ga ‘yan Nijeriya

Jagoran adawar Najeriya, ya nemi gaggauta yi wa tsarin mulkin ƙasar gyaran fuska, don hana kotuna abin da ya kira “fakewa a bayan gaza bin ƙa’idojin shigar da ƙara da muhawarorin shari’a masu rikitarwa, suna tabbatar da zaɓen sata da kuma yin zagon ƙasa ga zaɓen al’umma”.

Atiku Abubakar ya ce wajibi ne a mayar da zaɓe da tattara sakamako ta hanyar laturoni, su zama tilas a Najeriya.

Wannan, wani ɓangare ne na taron manema labarai da shugaban adawar, kuma ɗan takarar jam’iyyar PDP a zaɓen 2023, ya gabatar ranar Litinin a Abuja. Taron na zuwa ne kwana uku, bayan hukuncin kotun ƙoli da ya yi watsi da ƙararsa ta ƙalubalantar nasarar Shugaba Bola Ahmed Tinubu.

Kotun dai ta yi watsi da ƙararrakin da Atiku Abubakar tare da takwaransa na jam’iyyar LP, Peter Obi suka ɗaukaka, inda ta ce ba su da ƙwararan hujjoji.

Atiku ya ce matsayin Kotun Kolin ko da yake, shi ne ƙarshe, amma dai ya bar baya da ƙura mai yawa.

Ya yi zargin cewa hukunce-hukuncen kotunan zaɓe, sun zaizaye yardar da ‘yan Najeriya ke da ita, ga tsarin zaɓe da kuma dimokraɗiyyar Najeriya.

Ya ce yana mamakin wanda zai shawo kan miliyoyin ‘yan Najeriya, su fita su yi zaɓe nan gaba, bayan sun bi layi sun yi rijista bisa tabbacin da INEC ta ba su, amma sai suka ga an sace ƙuri’unsu, tare da bai wa waɗanda ba su zaɓa ba, nasara.

Dan adawan ya ce idan mutane suka daina yarda, kuma suka dawo daga rakiyar zaɓuka, dimokraɗiyya ta durƙushe ke nan. Kuma ta hanyar tabbatarwa da halasta ci gaba da rashin gaskiya a zaɓuka, kotunan Najeriya, na ƙwace ‘yancin masu zaɓe, na zaɓar wa kansu shugabanni.

Ita dai hukumar zaɓe ta ce ta yi zaɓe cikin gaskiya da adalci, kuma sakamakon hukunce-hukunce da aka yanke a kotuna sun nuna cewa INEC ta taka rawar gani.

PRNigeria haus

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
https://nnn.ng/image-compressor/
Latest News
Mutane 6 Sun Rasu 4 Sun Jilkata Sanadiyyar Tsawa a Jihar AdamawaMatatar Dangote ta Dakatar da Amfani da Naira Wajen Sayar da Man FeturZaɓen 2027: Jam'iyyar ADC ta Mayar da Martani kan Hukuncin Kotu Akwai Yiwuwar ba zan kai Lokacin Zaɓen 2027 ba - ObiHukuncin da Kotu ta Yanke wa Direban Keke Napep Kan Aikata Fyaɗeɓata Sunan Gwamnatin Katsina: Kotu ta buƙaci Ƴan Sanda su Tsare Dr Kurfi Gwamnonin Arewacin Najeriya sun Kafa Gidauniyar Yaƙi da Matsalar TsaroGwamnatin Tarayya ba ta Yanke Hukuncin Sauya Kayan NYSC ba - Ministan MatasaJuyin Mulki: DSS ta Gurfanar da Mutane 5 kan ɓoye Timipre Sylva Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 2 Tare da Limami a Jihar Sokoto Dakarun Soji Sun Bankaɗo Wajen ƙera da Rarraba Bindigogi ga Ƴan Ta'addaJami'an DSS Sun Kama Tsohon Ministan Kimiyya da Fasaha, Uche NnajiYan Bindiga Sun Hallaka Mutane 10 a Jihar BenueNMDPRA ta Gargaɗi Gidajen Man da ba su Rage Farashi ba NECO: ɗalibai 35 na Hannun Ƴan Bindiga - Ƴan Sanda 
X whatsapp