Home Labarai CBN ya musanta sake fasalin kudin Nijeriya

CBN ya musanta sake fasalin kudin Nijeriya

Babban Bankin Najeriya ya ce ba shi da wani shiri na sake kirkiro sabbin takardun naira a shekara mai zuwa.

Wata sanarwa da daraktan sadarwa na Bankin Najeriya, Isa Abdulmumin ya fitar ranar Talata, ta bukaci ‘yan Najeriya su yi watsi da wani takaitaccen sakon waya da ake yadawa, wanda ke nuna cewa CBN na shirin sake bullo da sabbin takardun naira a shekara ta 2024. Takardar sanarwa ta bayyana cewa sakon ba haka yake ba.

“Mun shiga damuwa game da wannan batu, wanda muka musanta tun ba yanzu ba, amma ga alama yana samun karbuwa da muhawara masu yawa a kan illar irin wannan manufa ga tattalin arzikin Najeriya.

CBN ya ce “Muna son jaddada cewa bayanin da ke cikin wannan sako, ba haka yake ba”. Ya kara da cewa masu wallafa sako a yunkurinsu na jamhuru, sun jirkita rubutun daga wata tsohuwar manufa ta gwamnan CBN na baya a shekara ta 2007, amma sai suke bayyana shi tamkar yanzu ya faru.

Ya dai nanata cewa a yanzu babu wani shiri na sake fasalin takardun kudin kasar.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp