Home Labarai Tinubu ya Amince da nadin mai bashi shawara kan masu bukata ta...

Tinubu ya Amince da nadin mai bashi shawara kan masu bukata ta musamman

Shugaban ƙasar Nigeria Bola Tinubu ya amince da nadin Muhammad Abba Isa a matsayin babban mataimaki na musamman ga shugaban kasa kan harkokin masu bukata ta musamman.

A cewar wata sanarwa da mai ba shugaban kasa shawara na musamman kan harkokin yada labarai Ajuri Ngelale ya fitar a ranar Alhamis, yace nadin na cikin kudirin Tinubu na tabbatar da cewa kowane bangare na al’umma ya samu isasshiyar dama a gwamnatin sa.

“Muhammad Abba Isa fitacce ne wanda ya kwashe sama da shekaru 10 yana bada shawarwarin yadda za’a inganta rayuwar Masu bukaci ta musamman a gida Nigeria da kasashen waje,” in ji sanarwar.

“Sabon mai taimaka wa shugaban kasa ya kammala karatunsa kan harkokin mulki a jami’ar Maiduguri, inda kuma yayi Digirin na biyu a wannan fannin a dai jami’ar ta Maiduguri a shekarar 2017.

Shugaban ya bukaci sabon mai bashi shawara da ya samar da hanyoyin da za a bi don shigar da masu bukata ta musamman cikin manufofi da shirye-shiryen dukkan ma’aikatu, sassan da hukumomin gwamnatin tarayya tare da yin aiki kafada da kafada da kananan hukumomi don aiwatar da shirin, don inganta rayuwar su.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Shin AtikuObi Zasu Iya Tsige TinubuShettima a 2027? Daga Yushau A. ShuaibYadda Shari'ar Masarautar Kano ke Ci gaba da Wakana a Kotun ta ƙoliTawagar Amurka na Shirin Tafiya Pakistan Domin Tattaunawar Sulhu da IranDole Najeriya ta Samu Tsaro ta Kowane Hali - Babban Hafsan TsaroChelsea da Newcastle na Harin Coulibaly, Liverpool na Neman Siyan Marcos SensiBadaƙalar $1.3m: Kotu ta ba EFCC izinin Kama Tsohuwar Ministar jin ƙan Najeriya Sadiya FarouqRaphinha ya Magantu kan Fitar da ƙungiyarsa da aka yi Daga Champion LigRundunar sojin Najeriya ta Musanta bai wa Tsofaffin Mayaƙan Boko Haram MakamaiGwamnatin Tarayya ta Sauya Zarge-Zargen da ta ke yi wa MalamiAn Binne Birgediya Janar Braimah da Sauran Sojojin da Boko Haram ta KasheYaƙin Iran: Hauhawar farashin Kaya a Najeriya ya ƙaruAdadin Matasa 'Yan kwaya da Muka Kama a Shekara 5 - NDLEAJam'iyyar ADC ta Kori Nafi'u Bala GombeRigakafin ƙyanda ya Ceci Yara Miliyan 20 a Afirka - Hukumar Lafiya ta Duniya2027 Ita ce Dama ta ƙarshe da zan Fito Takara - Atiku
X whatsapp