Rundunar sojin Nijeriya ta yi nadamar kai harin kan masu Maulidi

Miscalculated Bombardment of Kaduna Civilians Regretted – Nigerian Military

Rundunar Sojojin Nijeriya ta bayyana harin da jirgin ta ya kai kan masu gudanar da taron mauludi a kauyen Ligarma dake jihar kaduna matsayin kuskure.

daraktan yada labaran rundunar, Manjo Janar Edward Buba, ne ya bayyana hakan ta cikin wata sanarwa da ya fitar ranar talata, inda sanarwa tace dakarun na sintirin kawar da ‘yan ta’addan sun hangi giftawar ‘yan ta’addan a kauyen.

yace na’urar sintirin ta hango zirga-zirga wasu mutane da suka yi kama da ‘yan ta’adda wannan ce ta sanya aka kai harin.

“an kai harin ne domin gani an dakile yunkunrin ‘yan ta’adda na gudanar da ayyukan su na ta’addanci kan fararen hula.”

yace dakarun sojojin na yin iyaka kokarin su wajen rarrabe al’ummar gari da ‘yan ta’adda. “sojojin na kallon rasa ran dukkan farar hula matsayin abin ki a duk lokacin da irin wannan ta auku.

Buba yace dakarun sojojin na daukar matakan da suka dace wajen kaucewa rasa rayukan fararen hula, daga cikin su kuwa harba bayar da umarnin da Al’umma dake rayuwa a yankunan dake fuskantar matsalar ‘yan ta’addan na su sanar da sojojin.

PRNigeria Hausa

Kidnapped School Children

Yauri FGC Students, Kebbi
1190 days 11 hours 45 minutes 50 seconds,

Baptist School Students, Kaduna
1172 days 13 hours 27 minutes 15 seconds

Tegina Islamiya Pupils, Niger (Freed)
Spent 88 days from May 30, 2021 - August 26, 2021


Report By: PRNigeria.com

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com