Home Labarai harin ta’addanci ya hallaka Mutane sama 160 a jihar Filato

harin ta’addanci ya hallaka Mutane sama 160 a jihar Filato

Wasu hare-haren ‘yan bindiga kan kauyuka sun yi sanadiyya mutuwar a kalla mutane 160 a tsakiyar Nijeriya a cewar mahukunta ranar litinin.

Adadin ya karu kan rahoton da rundunar sojin kasar ta fitar na cewa mutane 16 ne suka mutu a bias wani rikicin kabilanci da aka kwashe shekaru ana gudanarwa.

A yayin da yake ganawa da kamfanin dillancin labarai na AFP shugaban karamar hukumar Bokkos, a jihar Filato, Monday Kassah ya ce an tabbatar da mutuwar mutane 113 a daren litinin.

Yace yan bindigar sun kai hari a kalla garuruwa 20 ma bambanta, inda suka taba gidajen al’ummar dake rayuwa a garuruwan a cewar, Kassah.

“Mun samu mutane sama da 300 da suka jikka” wadanda yanzu haka an kaisu asibitocin Bokkos, Jos da barkin ladi.

Hukumar bayar da agajin gaggawa ta red cross ta ce mutane 104 ne suka mutu a kauyuka 18 na Bokkos.

Haka kuma an ruwato cewa mutane 50 ne suka mutu a kauyu mabambanta dake karamar hukumar barkin ladi, kamar yadda Dickson Chollom, guda cikin ‘yan majalisar jihar.

Dickson yayi Allah wadai da harin, inda ya bukaci jami’an tsaro su dauki matakin gaggawa kan lamarin.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a KatsinaJami'an Kwastam Biyu sun Rasa Ransu a Fafatawa da LakurawaMatar Aure ta Zuba wa Kishiyarta da 'Ya'yanta Biyu Fetur Tare da Banka Musu Wuta a KanoIna da ƴancin Mu'amala da Kowa ba Tare da La'akari da Jam'iyya ba - WikeAdadin Masu Fama da Cutar Tamowa na ƙaruwa a Najeriya - MSFGwamnatin Yobe ta Sha Alwashin Kawo ƙarshen Hare-Haren Boko Haram
X whatsapp