Home Labarai Lucky Aiyedatiwa ya karbi rantsuwa

Lucky Aiyedatiwa ya karbi rantsuwa

An rantsar da gwamnan Ondo na riƙo, Lucky Aiyedatiwa a matsayin cikakken gwamnan jihar, sa’o’i kadan mutuwar Rotimi Akeredolu sanadin cutar kansar jini .

Mataimakin gwamnan, ya karɓi ragamar mulkin jihar a matakin riƙo, bayan Gwamna Rotimi Akeredolu ya aika wasiƙa ga majalisar dokokin jihar don sanar da ita game da ƙudurinsa na tafiya jinya da kuma miƙa ragamar mulkin jihar ga Lucky Aiyedatiwa.

Alƙalin alƙalan jihar Mai shari’a Olusegun Odusola ne ya rantsar da shi a ofishin gwamnan Ondo dake ciki birnin Akure.

Idan za’a Iya Tunawa Dai tun da farko, an yi ta dambarwa a fagen siyasar jihar, lokacin da majalisar dokokin Ondo ta fara yunƙurin tsige Lucky Aiyetadiwa daga kan kujerar mataimakin gwamna.

Sakataren gwamnan jihar da kwamishinonin Ondo da shugaban jam’iyyar APC da alƙalan jihar na cikin manyan jami’an da suka halarci taron rantsuwar.

PRNigeria hausa

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp