Home Labarai Ƴan sanda sun kuɓutar da malamin jami’ar jihar Nasarawa

Ƴan sanda sun kuɓutar da malamin jami’ar jihar Nasarawa

Rundunar ƴan sanda a jihar Nasarawa ta ce sun ceto wani malamin jami’ar jihar da ke Keffi, Isaac Igbawua daga hannun masu garkuwa da mutane domin karbar kudin fansa.

wannan na kunshe ne cikin wata sanarwa da kakakin ƴan sandan jihar, Ramhan Nansel ya fitar aka kuma raba manema labarai

Ya ce jami’an rundunar ce tare da haɗin gwiwar ƴan bijilanti suka kuɓutar da malamin a wani kauye mai suna Ogba, a karamar hukumar Nasarawa Eggon da ke jihar.

An sace Igbawua, wanda malami ne a sashin kimiyyar ƙananan halittu (Microbiology) ranar 27 ga watan Disamba a karamar hukumar Kokona.

Kwana guda bayan sace shi, rundunar ƴan sandan jihar ta Nasarawa ta kama wani ɗalibin Jami’ar Tarayya da ke Lafiya, Daniel Favour Chukwuebuka, tare da kwato bindiga da harsashi a wajen da yake zama.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 200 Sun Mutu Sakomakon Girgizar ƙasar a ColombiaShahararren Mawaƙin Najeriya, Davido ya Rubuta wa Trump Wasiƙa Kan Zaɓen Jihar OsunHukumar NHRC ta Buƙaci a Kama Malamin Addinin, Sheikh JingirRundunar sojin Najeriya ta Daƙile Shirin Ƴan Bindiga a FilatoJami'an Ƴan Sanda 10 Sun Mutu Yayin Artabu da Ƴan Bindiga a Jihar KebbiAn Naɗa ɗan Najeriya Gidado Shuaib Wakilin Matasa na IPRA-UN Gabanin GWAEFCC da "Wuce Gona da Iri" da Tambayar 2027: Shin ana Rudar da Tinubu ta Hanyar Mutanen da ke Kewaye da Shi ? Daga Yushau A. ShuaibAn Samu Gawar Yara 3 da guda 1 a Sume a Gidan Mai Maganin GargajiyaMene ne Ainihin Abin da ya faru Aka Rufe Asusun Bankunan Gwamnatin Osun ?Jami'an Tsaro Sun Ceto Mutane 308 a Jihohin Arewacin Najeriya An Kama Mutane 6 da Ake Zargin da Taimaka wa Mayaƙan ISWAP a Jihar BornoZaɓen 2027: PDP ta Miƙa Sunan Jonathan ga INEC a Matsayin ɗan Takararta na Shugaban ƙasaIyanen Babban Jami'in Kula da Harkokin Kuɗaɗen ƙungiyar ISWAP Sun Miƙa Wuya ga SojojiAna Zargin Mayaƙan Boko Haram da Kashe Sojojin Nijar 14Gombe 2027: Malamai da Mambobin APC Sun yi Allah-wadai da Sukar Rarara ga Pantami
X whatsapp