Home Labarai Tinubu ya maye gurbin TSA da CRF

Tinubu ya maye gurbin TSA da CRF

Gwamnatin Shugaba Bola Tinubu ta rufe asusun ajiyar kudi na kasa wato (TSA) da gwamnatin Muhammadu Buhari ta yi amfani da shi wajen tara kudaden shiga.

Sai dai gwamnatin tarayya ta umurci dukkan ma’aikatu, da hukumomi da su tura kashi 100 na kudaden shiga zuwa asusun ajiyar kudaden shiga na yau da kullun, wani bangare na asusun tattara kudaden shiga (CRF).

CRF shine sabon asusu inda a yanzu gwamnatin Tinubu za ta karba tare da hada kudaden shigarta a cikin sa.

Hakan ya zo ne bisa wata takardar mai kwanan watan 28 ga Disamba, 2023, wadda ma’aikatar kudi ta fitar a ranar Talata, 2 ga Janairu, 2024.

Wannan umarni dai ya rufe asusun baitul mali na bai daya da tsohuwar gwamnatin Muhammadu Buhari ta yi amfani da shi.

PRNigeria hausa

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a KatsinaJami'an Kwastam Biyu sun Rasa Ransu a Fafatawa da LakurawaMatar Aure ta Zuba wa Kishiyarta da 'Ya'yanta Biyu Fetur Tare da Banka Musu Wuta a KanoIna da ƴancin Mu'amala da Kowa ba Tare da La'akari da Jam'iyya ba - WikeAdadin Masu Fama da Cutar Tamowa na ƙaruwa a Najeriya - MSFGwamnatin Yobe ta Sha Alwashin Kawo ƙarshen Hare-Haren Boko Haram
X whatsapp