Home General ‘Yan Bindiga sun hallaka mutane 10 a jihar Katsina

‘Yan Bindiga sun hallaka mutane 10 a jihar Katsina

Taswirar Katsina

Ƴan bindiga sun afkawa kauyen Kukar Babangida da ke karamar hukumar Jibia ta jihar Katsina, inda suka hallaka dagacin kauyen Magaji Haruna da ɗansa.

manema labarai a kasar sun ruwaito cewa an kuma kashe wasu mutum takwas a harin da aka kai da misalin karfe 10 na dare ranar Laraba.

Har ila yau, wani mazaunin garin ya bayyana cewa an tafi da mata wanda ba a san adadinsu ba zuwa yanzu.

Mazauna garin sun yi imanin cewa akwai manyan shugabannin ƴan bindiga biyu da ke cin karensu babu babbaka a ciki da wajen karamar hukumar ta Jibia.

Ƙauyen Kukar Babangida ya kasance ɗaya daga cikin kauyuka da ke fama da matsalar ƴan bindiga tun bayyanar ayyukansu a faɗin jihar.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Dangote ya ƙara farashin man feturHukumar Jin dadin alhazan Kano ta sanar da ranar fara jigilar maniyatantaYadda Lakurawa suka kashe masallata a KebbiDSS ta kama jagoran ISWAP da ake nema ruwa a jallo a EdoBa mu taɓa goyon bayan musguna wa Kristoci ba - Gwamnatin NajeriyaGobara ta tashi a babban kasuwar Fika da ke jihar YobeWaye Tunji Disu: Sabon Babban Sifeton 'Yansandan NajeriyaNijar ta amince da kundin ayyukan AES na shekara ta biyuAtiku ya zargi gwamnatin Tinubu da yi wa dimokuraɗiyya zagon ƙasaGwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanci
X whatsapp