Home Labarai EFCC zata cigaba da bincikar wasu Tsoffin Gwamnonin Nijeriya

EFCC zata cigaba da bincikar wasu Tsoffin Gwamnonin Nijeriya

Hukumar EFCC ta sake waiwayar binciken halasta kuɗaɗen haram na wasu tsofaffin gwamnoni 12 da wasu ministoci da suka gabata, kuma adadin kuɗin ya haura naira biliyan 853.b.

Jaridar Punch ta gano cewa adadin kuɗin da ake nema daga wajen wasu manyan tsofaffin minisrtoci da gwamnoni ya kai naira bilyan 772.2, kuma a yanzu haka EFFC na ci gaba da bincike kan naira bilyan 81.6 wanda ake tsammanin an sace su a ma’aikatar agajin gaggawa da yaki talauci.

Kazalika, kazalika ana zargin wasu dala biliyan biyi da ake zargin sun bata ta hanyar halasta kuɗin haram, wadanda ake tsammanin an karkatar da su ne a baya-bayan nan.

Akwai kuma dala biliyn 2.2 da ake zargin tsohon mai baiwa shugaban ƙasa shawara kan harkokin tsaro Sambo Dasuki ya karkatar da su, da mai gidajen yaɗa labara nan da ya rasu Raymond Dokpesi; da tsohon gwamnan Sokoto Attahiru Bafarawa: Tsohon ministan kudi Bashir Yuguda da sauransu.

A cewar EFCC kudaden an ware su ne domin sayan makamai da za su taimakwa yaƙin da ake da ‘yan tada ƙayar baya, amma aka sace su aka karkatar da sy aka kashe ba ta hanyar da ta dace ba.

Yayin da Dasuki ke a tsare a DSS a 2015, EFCC ta kama Dokpesi da Bafarawa da Yuguda da dai sauransu..

PRNigeria hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a KatsinaJami'an Kwastam Biyu sun Rasa Ransu a Fafatawa da LakurawaMatar Aure ta Zuba wa Kishiyarta da 'Ya'yanta Biyu Fetur Tare da Banka Musu Wuta a KanoIna da ƴancin Mu'amala da Kowa ba Tare da La'akari da Jam'iyya ba - WikeAdadin Masu Fama da Cutar Tamowa na ƙaruwa a Najeriya - MSFGwamnatin Yobe ta Sha Alwashin Kawo ƙarshen Hare-Haren Boko Haram
X whatsapp