Sojojin Nijeriya sun tarwatsa maboyar masu garkuwa da mutane a Taraba

Rahotannin daga Nijeriya na bayyana cewa dakarun rundunar sojin Najeriya tare da haɗin gwiwar wasu jami’an tsaro, sun lalata wata maboyar masu garkuwa da mutane tare da kuɓutar da mutum huɗu da aka yi garkuwa da su a yankin ƙaramar hukumar Yorro na jihar Taraba.

Cikin wata sanarwa da mai riƙon muƙamin daraktan yaɗa labaran rundunar sojin Najeriya ta 6 da ke jihar, Laftanar Oni Olubodunde ya sanya wa hannu, ya ce sojojin sun ƙaddamar da yaƙi da ‘yan bindigar ne tun da suka yawaita kai hare-hare a yankin ƙaramar hukumar.

Ya ƙara da cewa dakarunsu sun yi gumurzu da masu garkuwar a tsaunukan Gampu da na Ban Yorro, bayan musayar wuta tsakanin ɓangarorin ne, sai ‘yan bindigar suka arce inda suka bar mutum huɗu da suka yi garkuwa da su.

Sanarwar ta ƙara da cewa sojojin za su ci gaba da aiki a yankin har sai sun tabbatar da kuɓutar da sauran mutanen da ke hannun masu garkuwar.

PRNigeria Hausa

Kidnapped School Children

Yauri FGC Students, Kebbi
1189 days 4 hours 6 minutes 31 seconds,

Baptist School Students, Kaduna
1171 days 5 hours 47 minutes 56 seconds

Tegina Islamiya Pupils, Niger (Freed)
Spent 88 days from May 30, 2021 - August 26, 2021


Report By: PRNigeria.com

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com