Home Labarai Kotu a jihar Kano ta yanke hukuncin rataya ga dan Chaina da...

Kotu a jihar Kano ta yanke hukuncin rataya ga dan Chaina da hallaka Ummita.

Wata kotu a jihar Kano ta yanke wa ɗanƙasar China Frank Geng Quarong hukuncin kisa ta hanyar rataya saboda kashe budurwarsa, Ummukhulsum Sani Buhari.

Kwamishinan shari’a na jihar Kano, Haruna Dederi ne ya tabbatar wa BBC hukuncin kotun bayan zaman shari’ar da aka yi ranar Talata.

Ana zargin ɗanChina da daba wa marigayiyar wuƙa a gidansu da ke unguwar Janbulo a Kano, a ranar 16 ga Satumban 2022.

Laifin kisan ya saɓa da sashe na 221(b) na dokar ‘Penal Code’.

idan dai za’a iya tunawa tun lokacin tsohon gwamnan jihar Dr. Abdullahi Umar Ganduje, yasha Alwashin tabbatar da ganin shari’a ta yi aikinta a batun shari’a hallaka Ummulkhairi sani Buhari, matashiyar da dan Chaina ya hallaka.

Ya ce tuni suka sa aka kama mutumin da ake zargi Mista Geng Quanrong, bayan mutane sun damke shi a gidansu marigayiyar.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a KatsinaJami'an Kwastam Biyu sun Rasa Ransu a Fafatawa da LakurawaMatar Aure ta Zuba wa Kishiyarta da 'Ya'yanta Biyu Fetur Tare da Banka Musu Wuta a KanoIna da ƴancin Mu'amala da Kowa ba Tare da La'akari da Jam'iyya ba - WikeAdadin Masu Fama da Cutar Tamowa na ƙaruwa a Najeriya - MSFGwamnatin Yobe ta Sha Alwashin Kawo ƙarshen Hare-Haren Boko Haram
X whatsapp