Home Labarai Gwamnatin jihar Kebbi ta tabbatar da wawashe rumbun ajiyar abinci a jihar

Gwamnatin jihar Kebbi ta tabbatar da wawashe rumbun ajiyar abinci a jihar

Rahotanni daga jihar kebbi na bayyana yadda wasu mazaunan jihar suka auka cikin wani gidan ajiyar kaya na gwamnati a unguwar Bayan Kara cikin Birnin Kebbi, inda suka wawashe buhunhunan kayan abincin da ke ciki.

Mutanen waɗanda suka bijire wa jami’an tsaron da aka jibge a gidan ajiyar, sun kuma fasa wasu gidajen ajiyar kaya na ‘yan kasuwa da shagunan da ke yankin inda suka saci kayan abinci.

an ruwaito cewa zauna-gari-banzan sun kuma far wa wata babbar mota da aka laftawa kayan abinci dangin hatsi waɗanda aka yi niyyar rabawa a Birnin Kebbi.

Ta ce wawar kayan abinci a gidajen ajiyar kaya irin na Birnin Kebbi, ta faru a Abuja da garin Suleja a cikin jihar Neja.

Hakan na faruwa ne yayin da ake fama da matsalar tsadar rayuwa wanda galibi aka yi imani ya faru ne sanadin cire tallafin man fetur da barin naira ta ƙwaci kanta a kasuwar canji.

jaridar Dailytrust da ake wallafawa a Nijeriya ta ambato Muhammadu Gwadangwaji, shugaban ƙungiyar ‘yan kasuwar hatsi da ke Bayan Kara a Birnin Kebbi na cewa, “wasu matasa sun ma cinna wuta kan shaguna da gidajen ajiyar kayan ‘yan kasuwa a lokacin wawason.

“(Jami’an tsaro) sun harba harsasai da hayaƙi mai sa hawaye sama, amma su (matasan) ba su razana ba. Sun kutsa kai suka shiga ciki, sannan suka washe gidan ajiyar kayan gwamnati da wasu shagunanmu na ‘yan kasuwa”.

Da yake mayar da martani, Ahmed Idris, wanda shi ne babban sakataren yaɗa labarai ga Gwamna Nasir Idris, cewa ya yi lamarin “abin takaici ne”.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a KatsinaJami'an Kwastam Biyu sun Rasa Ransu a Fafatawa da LakurawaMatar Aure ta Zuba wa Kishiyarta da 'Ya'yanta Biyu Fetur Tare da Banka Musu Wuta a KanoIna da ƴancin Mu'amala da Kowa ba Tare da La'akari da Jam'iyya ba - WikeAdadin Masu Fama da Cutar Tamowa na ƙaruwa a Najeriya - MSFGwamnatin Yobe ta Sha Alwashin Kawo ƙarshen Hare-Haren Boko Haram
X whatsapp