Home Labarai Gwamnan Kano ya sake nada Oga Boye a mukami

Gwamnan Kano ya sake nada Oga Boye a mukami

Gwamnan jihar kano Alhaji Abba Kabir Yusuf ya sake yin sabbin nade-nade a cikin kunshin gwamnatin jihar.

Wannan na kunshe ta cikin wata sanarwa mai dauke da sa hannun daraktan yada labaran gwamnan Sanusi Bature Dawakin Tofa.

Sanarwar ta ayyana Farfesa Ibrahim Magaji barde matsayin mai bada shawara na musamman ga mai girma gwamna fannin harajin cikin gida.

  1. Dr. Abdulhamid Danladi, mai bawa Gwamnan shawara kan ‘yan kano mazauna ketare na II
  2. Engr. Bello Muhammad Kiru, Mai bada shawara na musamman fannin Albarkatun ruwa.
  3. Yusuf Shuaibu Imam (Ogan Boye) da aka sake nadawa matsayin Mai bada shawara na Musamman kan matasa da wasannan.
  4. Sai kuma Dr. Nura Jafar Shanono da aka matsar daga matsayin Mai bada shawara na musamman a fannin Albarkatun ruwan, zuwa babban managan hukumar (WRECA).
  5. haka kuma sanarwa ta bayyana daga likkafar Hon. Baba Abubakar Umar daga mai bada shawara na musamman zuwa babban sakataren hukumar dake lura da makarantu masu zaman kansu na jihar kano.
  6. An kuma nada Hon. Nasir Mansur Muhammad a matsayin babban daraktan dake lura da kanana da matsakaitan sana’oi (SMEs)
  7. Aminu Hamidu Bako Kofar Na’isa zai zama mataimakin babbana daraktan (DMD), a ma’aikatar aikin gona da cigaban karkara ta (KNARDA).

haka kuma an nada Engr. Mukhtar Yusuf, matsayin mataimakin babban daraktan (DMD) a hukumar (WRECA).

Daga bisani sanarwar ta tabbatar da cewa nadin ya fara aiki nan take, tare da fatan kammalawa lafiya da nasara.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 200 Sun Mutu Sakomakon Girgizar ƙasar a ColombiaShahararren Mawaƙin Najeriya, Davido ya Rubuta wa Trump Wasiƙa Kan Zaɓen Jihar OsunHukumar NHRC ta Buƙaci a Kama Malamin Addinin, Sheikh JingirRundunar sojin Najeriya ta Daƙile Shirin Ƴan Bindiga a FilatoJami'an Ƴan Sanda 10 Sun Mutu Yayin Artabu da Ƴan Bindiga a Jihar KebbiAn Naɗa ɗan Najeriya Gidado Shuaib Wakilin Matasa na IPRA-UN Gabanin GWAEFCC da "Wuce Gona da Iri" da Tambayar 2027: Shin ana Rudar da Tinubu ta Hanyar Mutanen da ke Kewaye da Shi ? Daga Yushau A. ShuaibAn Samu Gawar Yara 3 da guda 1 a Sume a Gidan Mai Maganin GargajiyaMene ne Ainihin Abin da ya faru Aka Rufe Asusun Bankunan Gwamnatin Osun ?Jami'an Tsaro Sun Ceto Mutane 308 a Jihohin Arewacin Najeriya An Kama Mutane 6 da Ake Zargin da Taimaka wa Mayaƙan ISWAP a Jihar BornoZaɓen 2027: PDP ta Miƙa Sunan Jonathan ga INEC a Matsayin ɗan Takararta na Shugaban ƙasaIyanen Babban Jami'in Kula da Harkokin Kuɗaɗen ƙungiyar ISWAP Sun Miƙa Wuya ga SojojiAna Zargin Mayaƙan Boko Haram da Kashe Sojojin Nijar 14Gombe 2027: Malamai da Mambobin APC Sun yi Allah-wadai da Sukar Rarara ga Pantami
X whatsapp