Home Labarai Sojojin Saman Nijeriya sun sake hallaka Kwamandan ISWAP a Jihar Borno

Sojojin Saman Nijeriya sun sake hallaka Kwamandan ISWAP a Jihar Borno

Nigeria Airforce

Wani harin dakarun sojin saman Nijeriya karkashin Operation Hadin kai (OPHK) yayi sanadiyyar tarwatsa maboyar mayakan kungiyar ISWAP a kauyen Kulleram dake yankin tafkin Chadi.

Wannan na kunshe ta cikin wata sanarwa da daraktan yada labarai da bayanai na rundunar sojin saman Nijeriya Air Vice Marshal Edward Gabkwet ya fitar mai dauke da kwanan wata 16 ga watan Afrilun 2024.

Sanarwar ta ce dakarun sun gudanar da harin ne a ranar 13 ga watan Afrilun 2024, wanda yayi sanadiyyar mutuwar mayakan masu tada kayar baya kimanin 30, wanda cikin su harda manyan kwamandoji da suka hadar da Ali Dawud, Bakura Fallujah, da Malla Ari.

Haka kuma yayin harin dakarun sun sami nasarar tarwatsa maboyar ‘yan ta’addan, baburan hawa da wasu kayan aikin ‘yan ta’addan masu tarin yawa.

Rahotannin sirri dake fitowa daga yankin na kulleram wanda ke matsayin  wata cibiyar hada-hada wanda ciki har da sarrafa kayan masarufi.

Sanarwar tace atisayen rundunar sojin saman ya nuna yadda runudnar sojin ta mayar da hankali wajen ganin ta kawar da  matsalolin rashin tsaro dake addabar Al’ummar Nijeriya.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Shin AtikuObi Zasu Iya Tsige TinubuShettima a 2027? Daga Yushau A. ShuaibYadda Shari'ar Masarautar Kano ke Ci gaba da Wakana a Kotun ta ƙoliTawagar Amurka na Shirin Tafiya Pakistan Domin Tattaunawar Sulhu da IranDole Najeriya ta Samu Tsaro ta Kowane Hali - Babban Hafsan TsaroChelsea da Newcastle na Harin Coulibaly, Liverpool na Neman Siyan Marcos SensiBadaƙalar $1.3m: Kotu ta ba EFCC izinin Kama Tsohuwar Ministar jin ƙan Najeriya Sadiya FarouqRaphinha ya Magantu kan Fitar da ƙungiyarsa da aka yi Daga Champion LigRundunar sojin Najeriya ta Musanta bai wa Tsofaffin Mayaƙan Boko Haram MakamaiGwamnatin Tarayya ta Sauya Zarge-Zargen da ta ke yi wa MalamiAn Binne Birgediya Janar Braimah da Sauran Sojojin da Boko Haram ta KasheYaƙin Iran: Hauhawar farashin Kaya a Najeriya ya ƙaruAdadin Matasa 'Yan kwaya da Muka Kama a Shekara 5 - NDLEAJam'iyyar ADC ta Kori Nafi'u Bala GombeRigakafin ƙyanda ya Ceci Yara Miliyan 20 a Afirka - Hukumar Lafiya ta Duniya2027 Ita ce Dama ta ƙarshe da zan Fito Takara - Atiku
X whatsapp