Home Labarai Farashin Iskar Gas (LPG) ya sauko a Nigeria

Farashin Iskar Gas (LPG) ya sauko a Nigeria

 

Rahotanni daga Nijeriya na bayyana cewa farashin gas din girki (LPG) ya fara sauka a kasar sakamakon faduwar darajar dala da habakar darajar Naira a kasuwar kasar.

Idan dai za a iya tunawa a ‘yan tskanin nan AL’ummar Nijeriya suka koka kan yadda farashin Iskar gas din tayi tashi gwauron zabi, abin da suka bukaci mahukunta a kasar da su sanya baki domin ganin an sami sauki.

Ko dai a watan Maris din daya gabata an sayar da gas din na girki a kan farashin Naira 1,500 ko wannen (kg), sai dai sakamakon faduwar dalar a kasuwar chanjin Nijeriya yasa yanzu haka ake sayar da iskar gas din kan farashin Naira 1,100.

Jaridar Economic confidential ta rawaito cewa a wajen sayar da iskar Gas na Iju-ishaga dake jihar Legas ana sayar da iskar gas din naira 1,100 dukkan (kg) an sami ragi kan yadda aka sayar a watan Maris din daya gabata.

Ana dai sa ran farashin zai cigaba da sauka idan babban bankin kasar ya cigaba da kokarin da yake na farfado da darajar Naira a kasuwar chanji ta duniya, tare da sanya idanu kan ‘yan kasuwa wadan ake zargi da tsawwala AL’ummar kasar.

PRNigeria Hausa

 

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 200 Sun Mutu Sakomakon Girgizar ƙasar a ColombiaShahararren Mawaƙin Najeriya, Davido ya Rubuta wa Trump Wasiƙa Kan Zaɓen Jihar OsunHukumar NHRC ta Buƙaci a Kama Malamin Addinin, Sheikh JingirRundunar sojin Najeriya ta Daƙile Shirin Ƴan Bindiga a FilatoJami'an Ƴan Sanda 10 Sun Mutu Yayin Artabu da Ƴan Bindiga a Jihar KebbiAn Naɗa ɗan Najeriya Gidado Shuaib Wakilin Matasa na IPRA-UN Gabanin GWAEFCC da "Wuce Gona da Iri" da Tambayar 2027: Shin ana Rudar da Tinubu ta Hanyar Mutanen da ke Kewaye da Shi ? Daga Yushau A. ShuaibAn Samu Gawar Yara 3 da guda 1 a Sume a Gidan Mai Maganin GargajiyaMene ne Ainihin Abin da ya faru Aka Rufe Asusun Bankunan Gwamnatin Osun ?Jami'an Tsaro Sun Ceto Mutane 308 a Jihohin Arewacin Najeriya An Kama Mutane 6 da Ake Zargin da Taimaka wa Mayaƙan ISWAP a Jihar BornoZaɓen 2027: PDP ta Miƙa Sunan Jonathan ga INEC a Matsayin ɗan Takararta na Shugaban ƙasaIyanen Babban Jami'in Kula da Harkokin Kuɗaɗen ƙungiyar ISWAP Sun Miƙa Wuya ga SojojiAna Zargin Mayaƙan Boko Haram da Kashe Sojojin Nijar 14Gombe 2027: Malamai da Mambobin APC Sun yi Allah-wadai da Sukar Rarara ga Pantami
X whatsapp