EFCC ta kama ‘yan damfara 28 a birnin Abuja

Hukumar yaki da masu yiwa tattalin arzikin kasa zagon kasa ta EFCC ta sami nasarara kama mutane 28 da ake zargi da Damfara a birnin tarayya Nijeriya Abuja.

Wannan ya biyo bayan wani simame da dakarun hukumar dake shiyyar birnin tarayya suka gudanar kan wadanda ake zargin da ayyukan damfarar ta yanar gizo.

Ta cikin wata sanarwa da sashin yada labarai da hulda da jama’a na hukumar ya fitar, yace an sami nasarar kama mutanen ne a yankin Gwarimpa da Katampe dake birnin bayan samun bayanai kan yadda suke gudanar da ayyukan na damfara.

Sanarwar ta kara da cewa dakarun sun sami wayoyin hannun guda 43 kirar kamfanoni da dama sai kuma abin hawa da kuma agoggunan zamani (Smart watches) a hannun wadanda ake zargin.

Daga bisani  hukumar ta tabbatar da shirin ta na gurfanar da su gaban kotu da zarar ta kammala bincike.

PRNigeria Hausa

Kidnapped School Children

Yauri FGC Students, Kebbi
1190 days 9 hours 8 minutes 44 seconds,

Baptist School Students, Kaduna
1172 days 10 hours 50 minutes 9 seconds

Tegina Islamiya Pupils, Niger (Freed)
Spent 88 days from May 30, 2021 - August 26, 2021


Report By: PRNigeria.com

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com