Home General Tinubu ya taya ‘yan Nijeriya murna cika shekaru 25 a tirbar Damukradiyya

Tinubu ya taya ‘yan Nijeriya murna cika shekaru 25 a tirbar Damukradiyya

Shugaban Najeriya Bola Tinubu ya ce gwamnatinsa tana cika alƙawurran da ta yi wa jama’ar kasar.

Tinubu wanda ya taya ƴan Najeriya murnar cika shekara 25 kan mulkin dimokuraɗiyya babu katsewa, ya kuma nemi haɗin kan al’umma domin samar da kyakkyawar ƙasa da za ta zamo abin alfahari ga ƴan baya.

Ya kuma yi gargaɗi a kan jefa dimokuraɗiyya cikin mawuyacin hali yana mai cewa “Dole mu ci gaba da haɗa kai wajen gina ƙasarmu da kuma jaddadawa a koda yaushe, cewa ba mu da wata ƙasa da ta fi Najeriya’’.

A wani jawabi da ya yi wa majalisar dokokin Najeriya, shugaba Tinubu ya nemi haɗin kan ƴan majalisar da ma sauran jama’ar ƙasar wajen ci gaba da aiwatar da manufofin gwamnatinsa da kuma bunƙasa Najeriya.

Shugaban Najeriyar ya kuma nemi goyon bayan majalisar wajen kammala aiki a kan kasafin kuɗin da ya gabatar mata, wanda ya ce zai taimaka wajen aiwatar da tsare-tsaren da gwamnati ke da su, masu muhimmanci ga jama’ar ƙasa.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp