Home General Kungiyoyin Kwadagon Nijeriya sun janye yajin aiki

Kungiyoyin Kwadagon Nijeriya sun janye yajin aiki

Manyan ƙungiyoyin ƙwadago biyu a Najeriya, wato Nigeria Labour Congress da kuma Trade Union Congress sun sanar da dakatar da yajin aikin da suka fara yi a ranar Litinin.

Ƙungiyoyin biyu sun sanar da wannan mataki ne bayan kammala tattaunawar shugabannin ƙungiyoyin biyu yau Talata, a Abuja.

Ƙungiyoyin ƙwadagon sun tsunduma yajin aiki ne bayan gaza cimma matsaya tsakaninsu da gwamnatin tarayya kan abin da zai zama albashi mafi ƙanƙanta ga ma’aikata a Najeriya.

Jim kaɗan bayan kammala taron, ƙungiyoyin ƙwadagon sun ce sun janye yajin aikin ne domin hanzarta tattaunawar da ake yi tsakanin su da gwamnati game da albashi mafi ƙanƙanta, wanda shi ne babban abin da ya janyo taƙaddamar.

Zaman da shugabannin NLC da TUC suka yi a ranar ta Talata ya mayar da hankali ne kan yarjejeniyar da aka cimma tsakanin ƙungiyoyin da gwamnatin a wata ganawa da suka yi ranar Talata tare da sakataren gwamnatin tarayya.

Yajin aikin dai ya taɓa ɓangarori daban-daban na tattalin arziƙin Najeriya, ɗaya daga ciki shi ne katsewar lantarki a faɗin ƙasar.

Tun farko, a ranar Talata ƙungiyar ta bayyana cewa za ta ci gaba da yajin aikin har sai shugabannin ƙungiyar sun kammala tattaunawa kan yarjejeniyar da aka cimma tsakanin ƙungiyar da gwamnati.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a KatsinaJami'an Kwastam Biyu sun Rasa Ransu a Fafatawa da LakurawaMatar Aure ta Zuba wa Kishiyarta da 'Ya'yanta Biyu Fetur Tare da Banka Musu Wuta a KanoIna da ƴancin Mu'amala da Kowa ba Tare da La'akari da Jam'iyya ba - WikeAdadin Masu Fama da Cutar Tamowa na ƙaruwa a Najeriya - MSFGwamnatin Yobe ta Sha Alwashin Kawo ƙarshen Hare-Haren Boko Haram
X whatsapp