Home General Sojojin Nijeriya sun hallaka Dan Ta’adda Buharin Yadi

Sojojin Nijeriya sun hallaka Dan Ta’adda Buharin Yadi

Gwamnatin jihar Kaduna ta tabbatar da mutuwar shahararren dan ta’addan nan wanda ya addabi arewacin Nijeriya Buharin Yadi.

Wannan dai na kunshe ta cikin wata mai dauke da sa hannun kwamishinan tsaro da Al’amuran cikin gida na jihar Samuel Aruwan.

Wani barin wuta da dakarun sojojin Nijeriya na rundunar Operation Whirl Punch sukayi kan  maboyar dan ta’addan Buhari Alhaji Halidu wanda aka fi sani da (Alias Buharin Yadi) ta yi sanadiyyar mutuwar sa da wasu cikin mayakan sa a maboyar su.

Dakarun sojojin dake karkashin kwamandan sojoji dake lura da iyakar kananan hukumomin Giwa da Sabuwa dake Jihohin kaduna da Katsina Manjo Janar MLD Saraso, sun sami nasarar ne a daidai Idasu bisa wasu bayanan sirri da suka samu kan mayakan dake sintiri a yankunan Samunaka, saulawa dake jihar Katsina.

Bawan wani batakashi daya gudana tsakanin dakarun da mayakan bayan bankado maboyar su da dakarun sukayi abinda ya haddasa mutuwar shanu masu tarin yawa.

Kachalla buhari Alhaji Haladu wanda aka fi sani da Buharin Yadi ko kuma Buhari Janar da saran tawagar sun uzzirawa yankunan Kidandan/Galadimawa dake karamar hukumar, Sabon Birni/Kerawa dake karamar hukumar Igabi, Sabuwa dake jihohin Katsina Niger da Zamfara.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 200 Sun Mutu Sakomakon Girgizar ƙasar a ColombiaShahararren Mawaƙin Najeriya, Davido ya Rubuta wa Trump Wasiƙa Kan Zaɓen Jihar OsunHukumar NHRC ta Buƙaci a Kama Malamin Addinin, Sheikh JingirRundunar sojin Najeriya ta Daƙile Shirin Ƴan Bindiga a FilatoJami'an Ƴan Sanda 10 Sun Mutu Yayin Artabu da Ƴan Bindiga a Jihar KebbiAn Naɗa ɗan Najeriya Gidado Shuaib Wakilin Matasa na IPRA-UN Gabanin GWAEFCC da "Wuce Gona da Iri" da Tambayar 2027: Shin ana Rudar da Tinubu ta Hanyar Mutanen da ke Kewaye da Shi ? Daga Yushau A. ShuaibAn Samu Gawar Yara 3 da guda 1 a Sume a Gidan Mai Maganin GargajiyaMene ne Ainihin Abin da ya faru Aka Rufe Asusun Bankunan Gwamnatin Osun ?Jami'an Tsaro Sun Ceto Mutane 308 a Jihohin Arewacin Najeriya An Kama Mutane 6 da Ake Zargin da Taimaka wa Mayaƙan ISWAP a Jihar BornoZaɓen 2027: PDP ta Miƙa Sunan Jonathan ga INEC a Matsayin ɗan Takararta na Shugaban ƙasaIyanen Babban Jami'in Kula da Harkokin Kuɗaɗen ƙungiyar ISWAP Sun Miƙa Wuya ga SojojiAna Zargin Mayaƙan Boko Haram da Kashe Sojojin Nijar 14Gombe 2027: Malamai da Mambobin APC Sun yi Allah-wadai da Sukar Rarara ga Pantami
X whatsapp